Maras Hoto
Search

 
Jirgin Saman Fasinja Ya Fado Kan Mutane A Garin Goma A Kasar Kwango Ta Kinshasa

15/04/2008

faduwar Jirgi A Birnin GomaJami’ai a kasar Kwango ta Kinshasa sun ce mutane fiye da saba’in suka mutu a lokacin da wani jirgin saman fasinja ya fadi a birnin Goma dake gabashin kasar.

Jami’ai suka ce jirgin, kirar DC-9 yana dauke da mutane har 100 a lokacin da ya subuto kan wani wuri mai kasuwa ya kama da wuta jim kadan a bayan tashinsa yau talata. Suka ce mutane akalla 6 a cikin jirgin sun kubuta da rayukansu, cikinsu har da biyu daga cikin matuka jirgin.

Shaidu sunce da alamun akwai wadanda suka mutu daga cikin mutanen da jirgin ya fado a kansu.

Jami’ai suka ce jirgin na kamfanin safarar jiragen sama na Hewa Bora, ya doshi Kinshasa ne, babban birnin kasar. A makon jiya, Kungiyar Tarayyar Turai ta saka sunan kamfanin safarar jiragen saman Hewa Bora a cikin wadanda ta haramtawa jiragensu shawagi a kasashen Turai a saboda damuwa kan lafiyar jiragen nasu.

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin

  Muhimmin Labari
Taron Kolin Kasashen Afirka yayi Kiran Da A Kafa Gwamnatin Hadin Kan Kasa A Zimbabwe

  Karin Labarai
Kungiyar Tarayyar Kasashen Afirka Zata Fara Taron Koli Yau Litinin
Kwamitin Sulhun Majalisar Dinkin Duniya yayi Tur Da Cin Zarafin 'Yan Hamayya Da Ake Yi A Zimbabwe
Morgan Tsvangirai Ya Janye Daga Zaben Fitar Da Gwani Na Shugaban Kasa A Zimbabwe
Sojojin Gwamnatin Afghanistan Da Na NATO Su Na Yakar 'Yan Taliban A Kandahar
Sangandale Rabonta Ya Rantse  Audio Clip Available