Maras Hoto
Search

 
Fernando Lugo ya lashe zaben shugaban kasar da aka yi jiya lahadi a kasar Paraguay

21/04/2008

Dan takarar hamayya Fernando Lugo ya lashe zaben shugaban kasar da aka yi jiya lahadi a kasar Paraguay, abinda ya kawo karshen mulkin shekaru 61 da jam’iyyar Colorado ta yi.

 Lugo ya doke ’yar takarar jam’iyya mai mulki Blanca Ovelar, wadda jiya da daddare ta mika wuya ta ce ta sha kaye, ta kawo karshen yunkurinta na zamowa macen farko da zata zamo shugabar kasar.
Paraguay
Paraguay

Mr. Lugo yayi alkawarin tallafawa talakawan kasar. Shi dai Lugo tsohon babban fada na ’yan darikar Roman Katolika ne mai mukamin Bishop, kuma shine ya zamo dan takara na gamayyar jam’iyyun hamayya da suka hada da babbar jam’iyyar hamayyar kasar, da kungiyoyin kwadago, da kungiyoyin manoma da kuma Indiyawan daji. A can baya, mutane suna kiran Lugo da sunan Limamin Talakawa.

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin

  Muhimmin Labari
An Kama Radovan Karadzic

  Karin Labarai
Sabuwar Gasar Kacici-Kacici Ta 2008
Taron Kasashe Masu Arzikin Masana'antu Zai Mayar Da Hankali Kan Sauyin Yanayi Da Wasu Batutuwan
Taron Kolin Kasashen Afirka yayi Kiran Da A Kafa Gwamnatin Hadin Kan Kasa A Zimbabwe
Kungiyar Tarayyar Kasashen Afirka Zata Fara Taron Koli Yau Litinin