Maras Hoto
Search

Morgan Tsvangirai Ya Fasa Komawa Zimbabwe Asabar Din Nan

17/05/2008

Morgan Tsvangirai
Shugaban jam’iyyar hamayya ta kasar Zimbabwe ba zai koma gida kamar yadda ya shirya a yau asabar ba, a saboda dalilai na tsaro.

Wani kakakin jam’iyyar MDC ya ce sun samu bayani daga wata majiya mai tushe dangane da makarkashiyar da aka kitsa ta kashe Morgan Tsvangirai. Mr. Tsvangirai ya bar kasar Zimbabwe tun zaben shugaban kasa da na majalisar dokoki na ranar 29 ga watan Maris.

Sakamakon da hukuma ta bayar ya nuna cewa ya doke shugaba Robert Mugabe a zaben, amma bai samu fiye da rabin kuri’un da aka jefa, wanda ake bukata, don lashe zaben kai tsaye ba tare da yin zagaye na biyu ba.

Tun fari, an sa ran shugaban na jam’iyyar MDC zai koma daga kasashen Turai don fara yakin neman zaben zagaye na biyu na fitar da gwani da za a yi tsakaninsa da Mr. Mugabe ranar 27 ga watan Yuni. Jam’iyyar ta shirya wani gagarumin gangami gobe lahadi.

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin

  Muhimmin Labari
Yau Laraba  taron Jam’iyyar Republican zata ayyana tsaida dan takarar shugaban kasa John McCain,da matai makiyar sa Sarah Palin.

  Karin Labarai
Yau Talata Jam’iyyar Republican ta Amurka zata fara aiwatar da shirye shiryen taron ta na kasa gadan gadan
Ruwa na pantsama ya tsallaka  manyan katangu da aka gina a New Orleans
Barack Obama ya anshi zabin da jamiyyar sa ta democrat tayi masa na zama dan takarar shugaban kasa
A yammacin Alhamis din nan ne, dan takarar shugabancin Amurka na Jam’iyyar Democrat, Barack Obama,zaiyi na’am da tsaida shi dan takara
Hillary Clinton ta kirayi illahirin ‘Yan ‘Jam’iyyar Democrat, su marawa Obama
Michelle Obama, matar dan takaran jam’iyyar Democrat, ta  gayawa mahalarta taron cewa Obama zai zamar wa Amurka hazikin shugaba
Yau litinin dinnan abude babban taron Jam’iyyar Democrat a Denver, jihar Colorado
A daren yau Laraba  taron Jam’iyyar Republican zata ayyana tsaida dan takarar shugaban kasa John McCain,da matai makiyar sa Sarah Palin.
Tsohon firayim ministan kasar Pakistan ,Nawaz Sharif, ya yanke sabon lokacin dawo da manyan alkalan kasar
Jam’iyyar Democrat ta Amurka, a makon gobe, zatayi taron ta na kasa a Denver,Colorado.
Masana Kimiyya Sun Gano Kaburburan Mutanen Zamanin Da Cikin Hamadar Sahara A Nijar
Gasar Kacici-Kacici Ta 2008
Wani Maganin Tarin Fuka Yana Rage Karfin Maganin Kashe Kaifin Cutar Kanjamau
Yau Litinin Jacob Zuma Zai Bayyana Gaban Kotu A Afirka Ta Kudu
Steve Lucas Yayi Ban Kwana Da Muryar Amurka  Audio Clip Available
Hukumomin Kasar Chile Sun Sa Idanu Kan Wasu Duwatsu Biyu Masu Aman Wuta