Maras Hoto
Search

Morgan Tsvangirai Ya Janye Daga Zaben Fitar Da Gwani Na Shugaban Kasa A Zimbabwe

23/06/2008

Morgan TsvangiraiMadugun hamayya na kasar Zimbabwe, Morgan Tsvangirai, ya janye daga zaben fitar da gwani na ranar jumma'a mai zuwa inda aka shirya zai gwabza da shugaba Robert Mugabe, yana mai fadin cewa magoya bayansa za su jefa rayukansu cikin hatsari idan suka fito jefa kuri'a.

Mr. Tsvangirai ya bayyana wannan lahadi, 'yan sa'o'i kadan a bayan da dubban matasa 'yan tsagera masu goyon bayan Mr. Mugabe suka hana magoya bayan jam'iyyar hamayya ta MDC hallara domin gudanar da gangamin yakin neman zabe a Harare, babban birnin kasar.

Mr. Tsvangirai yayi watsi da zaben a zaman haramtacce, kuma kazamin yunkurin yin rufa ido, yana mai zargin magoya bayan shugaba Mugabe da laifin kashe magoya bayan jam'iyyar hamayya ta MDC su tamanin da shida cikin 'yan makonnin nan.

Ba a dai ji martani daga bakin Mr. Mugabe nan take ba, amma ministan shari'a na Zimbabwe, Patrick Chinamasa, ya ce Mr. Tsvangirai ya janye ne a saboda ta tabbata cewa zai sha kaye.

haka kuma, jami'ai sun bayyana cewa za a gudanar da zaben kamar yadda aka shirya har sai Mr. Tsvangirai ya sanar da hukumar zabe cewa ya janye.

Mr. Tsvangirai ya ce a ranar laraba zai bayyana matakin da zai dauka a nan gaba.

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin

  Muhimmin Labari
Yau Laraba  taron Jam’iyyar Republican zata ayyana tsaida dan takarar shugaban kasa John McCain,da matai makiyar sa Sarah Palin.

  Karin Labarai
Yau Talata Jam’iyyar Republican ta Amurka zata fara aiwatar da shirye shiryen taron ta na kasa gadan gadan
Ruwa na pantsama ya tsallaka  manyan katangu da aka gina a New Orleans
Barack Obama ya anshi zabin da jamiyyar sa ta democrat tayi masa na zama dan takarar shugaban kasa
A yammacin Alhamis din nan ne, dan takarar shugabancin Amurka na Jam’iyyar Democrat, Barack Obama,zaiyi na’am da tsaida shi dan takara
Hillary Clinton ta kirayi illahirin ‘Yan ‘Jam’iyyar Democrat, su marawa Obama
Michelle Obama, matar dan takaran jam’iyyar Democrat, ta  gayawa mahalarta taron cewa Obama zai zamar wa Amurka hazikin shugaba
Yau litinin dinnan abude babban taron Jam’iyyar Democrat a Denver, jihar Colorado
A daren yau Laraba  taron Jam’iyyar Republican zata ayyana tsaida dan takarar shugaban kasa John McCain,da matai makiyar sa Sarah Palin.
Tsohon firayim ministan kasar Pakistan ,Nawaz Sharif, ya yanke sabon lokacin dawo da manyan alkalan kasar
Jam’iyyar Democrat ta Amurka, a makon gobe, zatayi taron ta na kasa a Denver,Colorado.
Masana Kimiyya Sun Gano Kaburburan Mutanen Zamanin Da Cikin Hamadar Sahara A Nijar
Gasar Kacici-Kacici Ta 2008
Wani Maganin Tarin Fuka Yana Rage Karfin Maganin Kashe Kaifin Cutar Kanjamau
Yau Litinin Jacob Zuma Zai Bayyana Gaban Kotu A Afirka Ta Kudu
Steve Lucas Yayi Ban Kwana Da Muryar Amurka  Audio Clip Available
Hukumomin Kasar Chile Sun Sa Idanu Kan Wasu Duwatsu Biyu Masu Aman Wuta