Maras Hoto
Search

 
Har Yanzu Ana Dakon Sakamakon Zabe A Zimbabwe

28/04/2008

Lawyer for the opposition MDC (Movement for Democratic Change) Alec Muchadehama, outside the High Court in Harare, 08 Apr 2008
Lawyer for the opposition MDC (Movement for Democratic Change) Alec Muchadehama, outside the High Court in Harare, 08 Apr 2008
‘Yan kasar Zimbabwe su na dakon sakamakon zaben shugaban kasa da akayi cikin watan jiya, sakamakon da kafofin yada labaran kasar suka ce za a sake nan bada jumawa ba.

Wakilan hukumar zaben Zimbabwe sunce yau litinin, za a kammala sake kidaya kuri’u daga gundumomi ashirin da uku. Bayan kammala sake kidaya kuri’un ne jami’an suka ce za a gayyaci ‘yan takarar shugaban kasan ko wakilansu su tantance sakamakon zaben.

Kalaman daga shugaban hukumar zabe George Chiweshe, ya nuna cewa watakila hukumar ta gana da ‘yan takarar yau. Amma babu bayani kan anyi wannan taro zuwa sha biyun rana agogon Zimbabe. Kakakin Jam’iyyar ‘yan hamayya Nelson Chimasa ya gayawa Muriyar Amurka cewa Jam’iyyar bata da kwarin gwiwa kan sakamakon zabe da hukumar zata bayar.

Jam’iyyar MDC tace dan takarar ta Morgan tsvangirai ya doke shugaba Robert Mugabe a zaben shugaban kasa da akayi ranar 29 ga watan Maris. Hukumar zaben ta sha suka matuka daga kasashen duniya saboda kasa bayyana sakamakon zaben.

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin

  Muhimmin Labari
An Kama Radovan Karadzic

  Karin Labarai
Sabuwar Gasar Kacici-Kacici Ta 2008
Taron Kasashe Masu Arzikin Masana'antu Zai Mayar Da Hankali Kan Sauyin Yanayi Da Wasu Batutuwan
Taron Kolin Kasashen Afirka yayi Kiran Da A Kafa Gwamnatin Hadin Kan Kasa A Zimbabwe
Kungiyar Tarayyar Kasashen Afirka Zata Fara Taron Koli Yau Litinin