Maras Hoto
Search

Talakawan Burma Sun Shiga Tasku

08/05/2008

Ma’aikatan agaji da manema labarai a kasar Burma, sunce dimbin mutanen da guguwar Nargis ta nakasa a Burma, suna ketara kogin Irrawaddy, a fafutukar da suke yi ta neman abinci, ruwan sha da magunguna.

Shaidun gani da ido sunce sunga mutane suna kokawar karbar kayan agaji, a garuruwan da aka iya kaiwa, gefe guda kuma ga gawawwaki nan birjik a cikin kogin, suna yawo a kan ruwa.

A halin da ake ciki, Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Ban Ki-moon ya roki hukumomin kasar Burma da su yiwa Allah, su bada dama masu rabon kayan agaji su shiga kasar domin bayar da tallafi.

Shugaban Hukumar Kula da aikin agaji na majalisar Dinkin Duniya, John Holmes ya gaya wa manema labarai cewa zai yi kyau in da Burma zata janye ka’idojin bayar da takardun visar shiga kasarta, a kalla na wani dan lokaci. 

 Hukumomin Burma dai na shan suka kan yadda suke ki sassauta ka’idojin shiga ksarsu, al’amarin da ya kara jefa mabukata cikin mawuyacin hali. Saidai Holmes yace suna tattaunawa da gwamnati.

Sakatariyar harkokin Wajen Amurka Condoleezza Rice ma dai ta roki hukumomin na Burma da su kyale ma’aikatan agaji su kai dauki ga mabukatan cikin gaggawa.

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin

  Muhimmin Labari
Yau Laraba  taron Jam’iyyar Republican zata ayyana tsaida dan takarar shugaban kasa John McCain,da matai makiyar sa Sarah Palin.

  Karin Labarai
Yau Talata Jam’iyyar Republican ta Amurka zata fara aiwatar da shirye shiryen taron ta na kasa gadan gadan
Ruwa na pantsama ya tsallaka  manyan katangu da aka gina a New Orleans
Barack Obama ya anshi zabin da jamiyyar sa ta democrat tayi masa na zama dan takarar shugaban kasa
A yammacin Alhamis din nan ne, dan takarar shugabancin Amurka na Jam’iyyar Democrat, Barack Obama,zaiyi na’am da tsaida shi dan takara
Hillary Clinton ta kirayi illahirin ‘Yan ‘Jam’iyyar Democrat, su marawa Obama
Michelle Obama, matar dan takaran jam’iyyar Democrat, ta  gayawa mahalarta taron cewa Obama zai zamar wa Amurka hazikin shugaba
Yau litinin dinnan abude babban taron Jam’iyyar Democrat a Denver, jihar Colorado
A daren yau Laraba  taron Jam’iyyar Republican zata ayyana tsaida dan takarar shugaban kasa John McCain,da matai makiyar sa Sarah Palin.
Tsohon firayim ministan kasar Pakistan ,Nawaz Sharif, ya yanke sabon lokacin dawo da manyan alkalan kasar
Jam’iyyar Democrat ta Amurka, a makon gobe, zatayi taron ta na kasa a Denver,Colorado.
Masana Kimiyya Sun Gano Kaburburan Mutanen Zamanin Da Cikin Hamadar Sahara A Nijar
Gasar Kacici-Kacici Ta 2008
Wani Maganin Tarin Fuka Yana Rage Karfin Maganin Kashe Kaifin Cutar Kanjamau
Yau Litinin Jacob Zuma Zai Bayyana Gaban Kotu A Afirka Ta Kudu
Steve Lucas Yayi Ban Kwana Da Muryar Amurka  Audio Clip Available
Hukumomin Kasar Chile Sun Sa Idanu Kan Wasu Duwatsu Biyu Masu Aman Wuta