Koma Ga Shafi Mai Hoto

VOANews.com
News in 44 languages


 
Kanar Theoneste Bagosora Ya Ce Neman Bata Masa Suna Kawai Ake Yi

25/10/2005

Mutumin da ake zargin cewa shine ummul haba’isin kisan kare dangi da aka yi a kasar Rwanda a shekarar 1994 ya ce wannan zargi yunkuri ne kawai na neman bata masa suna.

A jiya litinin, Kanar Theoneste Bagosora, tsohon darektan ma’aikatar tsaro ta kasar Rwanda ya fara bayar da shaida a gaban Kotun bin Kadin laifuffukan yaki ta Majalisar Dinkin Duniya dake zama a kasar Tanzaniya.

Kanar Bagosora ya musanta kitsa kashe mutane dubu 800 ’yan kabilar Tutsi da masu tausaya musu daga cikin ’yan kabilar Hutu a madadin gwamnatin Rwanda. Masu gabatar da kararraki suka ce Kanar Bagosora ya umurci kwamandojin soja da su fara karkashe ’yan kabilar ta Tutsi jim kadan a bayan da shugaba Juvenal Habyarimana ya mutu a faduwar jirgin sama a watan Afrilun 1994.

Ana tuhumar Kanar Bagosora tare da wasu hafsoshin soja uku (Birgediya Janar Gratien Kibiligi, da Kanar Anatole Nsengiyumva da kuma Manjo Aloys Ntabakuze) da aikata kashe-kashen kare dangi da kuma cin zarafin bil Adama.

Kwamitin Sulhun MDD shine ya kafa kotun ta bin kadin laifuffukan yakin Rwanda a watan Nuwambar 1994. ya zuwa yanzu, kotun ta samu mutane 22 da laifi ta kuma sallami wasu mutanen su uku.

Muhimmin Labari
Jami'an Sojan Iran Sun Ce An fara Wata Gagarumar Rawar Daji Ta Kare Kasa Daga Hari Ta Sama

Karin Labarai
Yau Litinin Majalisar Dinkin Duniya Zata Kaddamar Da Aiki Mafi Girma Na Rigakafin Cutar Shawara Da Ta Taba Yi
Kwallon Kafa Ya Haddasa Rikicin Diflomasiyya Tsakanin Masar Da Aljeriya
Somaliyawa 'Yan Fashi A Teku Sun Sake Kai Hari Kan Wani Jirgin Ruwan Amurka Da Suka Taba Kamawa
Yau Alhamis Za A Rantsar Da Shugaba Hamid Karzai Na Afghanistan