Koma Ga Shafi Mai Hoto

VOANews.com
News in 44 languages


 
'Yan Tawayen Ivory Coast Sun Ce Ba Su Yarda Shugaba Laurent Gbagbo Yaci Gaba Da Zama Kan Wannan Kujera Ba

26/10/2005

Sojojin 'Yan Tawayen Ivory Coast
’Yan tawayen Ivory Coast sun yi watsi da kudurin Majalisar Dinkin Duniya, MDD, da ya kyale shugaba Laurent Gbagbo ya ci gaba da zama kan kujerarsa na karin shekara guda.

’Yan tawayen sun fada cikin sanarwar da suka bayar jiya talata cewa zasu dauki shugaba Gbagbo tamkar mutumin da yayi juyin mulki idan har ya ci gaba da zama kan karagar mulki bayan cikar wa’adin shugabancinsa yau laraba 26 ga watan Oktoba.

Wannan sanarwa ta ’yan tawaye ta zo a daidai lokacin da jam’iyyun adawa na kasar ta Ivory Coast suka ce zasu janye daga cikin gwamnatin hadin kan kasa idan har Mr. Gbagbo bai sauka daga kan kujerar shugabancin kasar ba.

A halin da ake ciki, rundunar sojojin kasar ta ce zata fara rufe gadojin dake Abidjan birni mafi girma a kasar, yayin da ake fargabar barkewar zanga-anga ta ’yan adawa.

Da farko an shirya gudanar da zabe ranar 30 ga watan Oktoba, amma sai aka dage har sai illa ma sha Allahu a saboda matsalolin da aka fuskanta wajen shirya zaben.

Kwamitin Sulhun MDD da kuma Kungiyar Tarayyar Kasashen Afirka duk sun amince da kyale Mr. Gbagbo ya ci gaba da zama kan kujerar shugabancin kasar na karin shekara guda har sai an gudanar da sabon zabe.

Muhimmin Labari
Jami'an Sojan Iran Sun Ce An fara Wata Gagarumar Rawar Daji Ta Kare Kasa Daga Hari Ta Sama

Karin Labarai
Yau Litinin Majalisar Dinkin Duniya Zata Kaddamar Da Aiki Mafi Girma Na Rigakafin Cutar Shawara Da Ta Taba Yi
Kwallon Kafa Ya Haddasa Rikicin Diflomasiyya Tsakanin Masar Da Aljeriya
Somaliyawa 'Yan Fashi A Teku Sun Sake Kai Hari Kan Wani Jirgin Ruwan Amurka Da Suka Taba Kamawa
Yau Alhamis Za A Rantsar Da Shugaba Hamid Karzai Na Afghanistan