Maras Hoto
Binciko Mini

 
An Fara Kidaya Kuri'u A Zaben Shugaban Kasa A Burkina Faso

14/11/2005

Shugaba Blaise Compaore na Burkina Faso
Shugaba Blaise Compaore na Burkina Faso
An rufe tasoshin zabe an kuma fara kidaya kuri'u a kasar Burkina Faso, inda masu jefa kuri'a a wannan kasa dake Afirka ta Yamma suka zabi shugaban kasa.

Shugaban hukumar zaben kasar, Moussa Michel Tapsoba, ya ce an gudanar da wannan zabe sumul. Ana sa ran za a dauki kwanaki da dama kafin a samu cikakken sakamako.

Ana sa ran cewa shugaba Blaise Compaore, mai neman wa'adi na uku a kan karagar mulki, zai lashe wannan zaben cikin sauki. Wasu 'yan takara na jam'iyyun hamayya sun soki tsayawar da yayi a wannan zabe, suna masu fadin cewa yin haka ta karya tanadin tsarin mulki cewar wa'adi biyu kawai mutum zai yi a kan mulki. Amma kuma wata kotu ta kyale shugaban da ya yi takara.

Mr. Compaore ya hau kan karagar mulki a sanadin juyin mulkin da yayi shekaru 18 da suka shige. An zabe shi ba tare da hamayya ba a 1991, aka kuma sake zabensa da gagarumin rinjaye a 1998.

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin
  Muhimmin Labari
Jami'an Sojan Iran Sun Ce An fara Wata Gagarumar Rawar Daji Ta Kare Kasa Daga Hari Ta Sama

  Karin Labarai
Yau Litinin Majalisar Dinkin Duniya Zata Kaddamar Da Aiki Mafi Girma Na Rigakafin Cutar Shawara Da Ta Taba Yi
Kwallon Kafa Ya Haddasa Rikicin Diflomasiyya Tsakanin Masar Da Aljeriya
Somaliyawa 'Yan Fashi A Teku Sun Sake Kai Hari Kan Wani Jirgin Ruwan Amurka Da Suka Taba Kamawa
Yau Alhamis Za A Rantsar Da Shugaba Hamid Karzai Na Afghanistan