Maras Hoto
Binciko Mini

 
Libya Ta Hana Bakin Haure Dubu Arba'in Tsallakawa Zuwa Turai A Wannan Shekarar

26/11/2005

Wani babban jami'in Libya ya ce kasarsa ta hana bakin haure fiye da dubu arba'in tsallakawa zuwa Turai a wannan shekara kawai.

Ministan harkokin cikin gida, Naser al-Mabrouk, shi ya bayyana wannan a birnin Rum a lokacin wani taron 'yan jarida na hadin guiwa da takwaran aikinsa na kasar Italiya, Giuseppe Pisanu.

Mr. Mabrouk yayi rokon da a samu hadin kan kasashen duniya wajen takalar matsalar bakin haure, ya kuma bayar da shawarar cewa ya kamata kasarsa ta dauki nauyin gudanar da taron kasashen duniya a kan wannan batu.

Bakin haure daga Afirka da Gabas ta Tsakiya sun mayar da Libya ta zamo zango mafi a'ala a yunkurinsu na tsallaka tekun bahar Rum zuwa cikin Turai domin neman ayyukan yi.

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin
  Muhimmin Labari
Kwallon Kafa Ya Haddasa Rikicin Diflomasiyya Tsakanin Masar Da Aljeriya

  Karin Labarai
Somaliyawa 'Yan Fashi A Teku Sun Sake Kai Hari Kan Wani Jirgin Ruwan Amurka Da Suka Taba Kamawa
Yau Alhamis Za A Rantsar Da Shugaba Hamid Karzai Na Afghanistan
Switzerland Ta Doke Nijeriya A Wasan Karshe Na Cin Kofin Kwallon Kafar Duniya Na Samari
Dan Kunar-Bakin-Wake Ya Kai Farmaki Kan Hukumar Leken Asirin Pakistan