Maras Hoto
Binciko Mini

 
'Yan Kasar Zimbabwe Suna Zaben 'Yan Majalisar Dattijai Asabar Din Nan

26/11/2005

Robert Mugabe<br />(File photo)
Robert Mugabe
(File photo)
Asabar din nan ne 'yan Zimbabwe suke zaben wakilan sabuwar majalisar dattijai, amma masu fashin bakin siyasa sun ce suna tsammanin akasarin masu jefa kuri'a miliyan uku da dubu dari biyu na kasar zasu kauracewa rumfunan zabe.

Masu fashin baki sun ce ko ohon masu jefa kuri'a da tsadar gudanar da bangaren majalisar dokoki da kuma fadar cikin gida a babbar jam'iyyar adawa ta "Movement for Democratic Change" sune zasu kashe guiwar masu jefa kuri'a su kauracewa zaben.

An samu baraka a cikin jam'iyyar MDC a bayan da ta jefa kuri'ar shiga cikin zaben. Shugaban jam'iyyar, morgan Tsvangirai, ya sa kafa ya shure wannan shawara, ya kuma kori 'ya'yan jam'iyyar su 26 wadanda suka ki jin kiran da yayi musu na su janye daga yin takara a zaben.

daya daga cikin wadanda suka kafa jam'iyyar ta MDC, Tendai Biti, ya ce ya kamata jam'iyyar ta kauracewa zaben, yana mai fadin cewa ba za a yi wannan zabe cikin adalci ba. Wadanda ke goyon bayan shiga zabe a cikin jam'iyyar sun bayyana fargabar cewa ta hanyar kauracewa zaben, za a kara mayar da jam'iyyar saniyar ware a harkokin siyasar kasar.

An kirkiro da sabuwar majalisar dattijan ne a bayan gyaran da aka yi ga tsarin mulkin Zimbabwe a cikin watan Maris.

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin
  Muhimmin Labari
Kwallon Kafa Ya Haddasa Rikicin Diflomasiyya Tsakanin Masar Da Aljeriya

  Karin Labarai
Somaliyawa 'Yan Fashi A Teku Sun Sake Kai Hari Kan Wani Jirgin Ruwan Amurka Da Suka Taba Kamawa
Yau Alhamis Za A Rantsar Da Shugaba Hamid Karzai Na Afghanistan
Switzerland Ta Doke Nijeriya A Wasan Karshe Na Cin Kofin Kwallon Kafar Duniya Na Samari
Dan Kunar-Bakin-Wake Ya Kai Farmaki Kan Hukumar Leken Asirin Pakistan