Maras Hoto
Binciko Mini

 
Hukumomin Islama A Somaliya Sun Ce Sun Kwace Babban Birnin Kasar Daga Hannun Mayakan Sojojin Sa Kai

05/06/2006

Mayakan Islama na Somaliya zaune kan wata mota dauke da bindigar harbo jiragen sama da suka kwace daga hannun abokan gabarsu
Mayakan Islama na Somaliya zaune kan wata mota dauke da bindigar harbo jiragen sama da suka kwace daga hannun abokan gabarsu
Hukumomin Islama a Somaliya sun ce sun ce sun kwace babban birnin kasar a bayan fadan makonni a tsakaninsu da mayakan wasu kungiyoyin sojan sa kai.

Shugaban Kotunan Islama a Mogadishu, Sheikh Sharif Sheikh Ahmed, ya bayyana samun nasara kan kawancen sojojin sa kan a lokacin wani jawabin da ya gabatar a rediyo litinin. Ya roki mazauna birnin da su yi na'am da sabbin shugabanninsu, yana mai fadin cewa kotunan su na kwadayin maido da zaman lafiya da tsaro a birnin.

Mayakan Islama masu alaka da kotunan Shari'a sun fatattaki mayakan sa kai daga wurare da dama da suka yi tunga a Mogadishu a cikin mako gudan da ya shige. Sun samu wata babbar nasarar ranar lahadi a lokacin da suka kwace garin Balad, suka tsinke hanyar samun kayan fada na kawancen sojojin sa kai.

An ce akasarin shugabannin kungiyoyin sojan sa kai na Mogadishu sun tsere daga birnin. Mazauna birnin suka ce mayakan kungiyoyin sun fara mika makamansu ga sojojin Islama.

An kashe mutane 350 a fadan da aka gwabza har sau uku a tsakanin bangarorin biyu tun daga watan Fabrairu.

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin
  Muhimmin Labari
Shugaba Umaru Musa 'Yar'aduwa Na Nijeriya Yana Fama Da Ciwon Kumburin Zuciya

  Karin Labarai
Yau Miliyoyin Musulmi Mahajjata Suke Hawan Arafat, Yayin Da Ruwan Sama Ya Kashe Mutane 11
Yau Fiye Da Wata Shida Ba A Biya Sojojin Kiyaye Zaman Lafiya Dake Somaliya Albashinsu Ba
Shugaba Barack Obama Zai Bayyana Sabuwar Manufarsa Kan Afghanistan A Ranar Talata
Jami'an Sojan Iran Sun Ce An fara Wata Gagarumar Rawar Daji Ta Kare Kasa Daga Hari Ta Sama