Maras Hoto
Search

 
Mutane Akalla Shida Sun Mutu A Tashe-Tashen Hankulan Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Kano

19/11/2007

Malam Ibrahim Shekarau
Malam Ibrahim Shekarau
Hukumomi a Jihar Kano dake arewacin Nijeriya sun ce an kashe mutane shida, wasu daruruwan kuma su na tsare a sanadin tashe-tashen hankula masu alaka da zaben kananan hukumomi a Jihar.

Kwamishinan 'yan sanda a Jihar ta Kano, Aminu Yusufu, ya ce tashin hankali ya barke a sanadin gardama tsakanin magoya bayan jam'iyyu dabam-dabam kan sakamakon zaben da ba hukuma ce ta bayar ba.

Kakakin 'yan sandan jihar, ya fadawa Sashen Hausa na Muryar Amurka cewa an kama mutane fiye da dari biyu da hamsin, dauke da muggan makamai.

Rahotanni daga yankin sun ce an tabka magudin zabe, har ma wasu 'yan takarar sun fara daukar matakan ganin an soke sakamakon wannan zabe. Wakilin Sashen Hausa na Muryar Amurka ya ji ta bakin tsohon gwamna Rabi'u Musa Kwankwaso, wanda yayi tattaki zuwa hedkwatar 'yan sanda domin yin korafi a madadin jam'iyyarsu ta PDP, cewa tun ma kafin a fara kidaya kuri'un, har an ayyana sakamakon wasu mazabu.

Amma kuma gwamna Ibrahim Shekarau ya ce ya gamsu da yadda aka gudanar da wannan zaben, sai dai bai ji dadin tashe-tashen hankulan da suka biyo baya ba. ya ce hukumomi su na bincike domin hukumta dukkan wadanda suke da hannu a lamarin.

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin

  Muhimmin Labari
An Kama Radovan Karadzic

  Karin Labarai
Sabuwar Gasar Kacici-Kacici Ta 2008
Taron Kasashe Masu Arzikin Masana'antu Zai Mayar Da Hankali Kan Sauyin Yanayi Da Wasu Batutuwan
Taron Kolin Kasashen Afirka yayi Kiran Da A Kafa Gwamnatin Hadin Kan Kasa A Zimbabwe
Kungiyar Tarayyar Kasashen Afirka Zata Fara Taron Koli Yau Litinin