Maras Hoto
Search

 
Hukumomin Italiya Da Na Netherlands Sun Bankado Gungun 'Yan Nijeriya Masu Fasa Kwabrin Mutane Da Safarar Kwayoyi

16/01/2008

Hukumomin kasashen Italiya da Netherlands ko Holland, sun ce sun wargaza wani gungun ’yan fasa-kwabri dake satar shigar da mutane zuwa kasashen Turai daga Afirka domin su tilasta musu yin karuwanci ko kuma safarar muggan kwayoyi.

Jami’ai sun fada jiya talata cewa sun kama ’yan Nijeriya 51 a kasar Italiya, suka kuma kama wasu 15 a kasar Netherlands. Suka ce mutanen sun tilasta ma mata ’yan Nijeriya yin aikin karuwanci, suka kuma yi amfani da wasu samari ’yan Nijeriya a zaman masu safarar kwayoyi.

Wani baturen ’yan sanda na kasar Italiya ya ce hukumomi sun kuma gano yadda ake magudin karbo yaran riko, inda wasu mata ’yan Nijeriya dake zaune a kasar Italiya suke dauko yara daga gidajen marayu a Nijeriya su je su saida su a kasashen waje. Hukumomin Italiya sun tuhumi wadannan mutanen da hada kai don aikata laifin safarar mutane, aikin bauta, satar mutane da fataucin muggan kwayoyi a tsakanin kasa da kasa.

Ministan harkokin cikin gida na Italiya, Giuliano Amato, ya yaba da aikin bankado wadannan miyagun mutane, yana mai fadin cewa an wargaza wannan gungu dake cin zarafin bil Adama.

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin

  Muhimmin Labari
Lamura Sun Fara Daidaituwa Jos Fadar Jihar Plateau, A Najeriya.

  Karin Labarai
Akalla Mutane talatin Sun Halaka A Iraqi.
Harin Kan Mumbai Ya Halaka Akalla Mutane 175, Ciki Har Da 'Yan Kasashen Ketare
Barack Obama Ya Bayyana Mutane Da Ya Nada Cikin Majalisar Tsaron Kasa.
A Thailand Jami'an Tsaro Zasu Yi Amfani Da Lalama.
Harin Kunar Bakin Wake A Iraqi Ya Kashe Mutane Tara Ya Jikkata Wasu Dama.
Jami'an Tsaron Indiya Sun Gano Gawarwakin Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Shugaban Amurka Mai Jiran Gado,Obama,Ya Nada Sabon Kwamiti Da Zai Bashi Shawara Kan Tattalin Arziki.
An Cimma Yarjejeniyar Daunin Iko A Somalia.
Sojoji Sun Isa Jos Domin Kwantarda Rikicin Siyasa.
Hadarin Motar Dakon Mai Ya Kashe Mutane Ashirin Da Biyar A Ghana.
'Yan Ta'adda Sun Kai Hari A India,Har sun Kashe Mutane Da Dama.
Farashin Mai Ya Fadi A Kasuwar New York A Hada-Hadar Yinin Talata.
'Yan Fashin Jirage A Somaliya Suna neman Diyyar Dala Milyan Biyu.
Majalisar Dinkin Duniya Tana Shirin Tallafawa 'Yan Gudun Hijira a Kwango.
'Yan ZAnga Zanga A Thailand Sun Hana Jiragen-sama Tashi.
Gurbataccen Maganin Fitar Hakori Ya Kashe Yara Ashirin Da Biyar A Najeriya.
Yau Litinin 'Yan Zanga Zanga A Thailand Sun Hana Majalisar Dokoki Yin Zama Ta Musamman.
Tashin Boma Bomai Uku Sun Kashe Akalla Mutane Goma Sha Tara A Iraqi.
Talata Za Fara Sabon Zagayen Taron Daunin Ikon Zimbabwe a Afrika Ta Kudu.
Mr.Obama Ya Zabi Babban Jami'i Mai Kula Da Ofishin Kasafin Kudi
'Yan Bindiga A Yanmkin Niger Delta Sun Kaiwa Kamfanin Shell Hari.
Shugaban Amurka Mai Jiran Gado Barack Obama, Zai Gabtarda Tawagawar Mutane Da za su Shugabanci Sashen Tattalin Arzikin Gwamnatinsa
Kungiyar al-Qaida Ta Yi Sako Ga Shugaban Amurka Mai Jiran Gado,Barack Obama.
'Yan Bindiga Sun Kai Hari A Wani Gari A Somalia Dake Dab Da Kan Iyakarta Da Kenya.
Kamfanin Safarar Jirage Ruwa Mafi Girma A Duniya Yace Zai Kaucewa Mashigin Ruwan Aden.
Obama Da McCain Sunyi Alkwari Zasu Yi Aiki Tare.
Rilwan Lukman Yana Cikin Jerin Sunayen Mutane Goma Sha Uku Da Shugaban Najeriya Ya Gabatarwa Majalisar Dattjiai Domin A Nadasu Ministoci.
Hukumar Kiyaye Hakkin Bi'adama Ta Majalisar Dinkin Duniya Tana Kira Ga Isra'ila Ta Janye Kawanya Datakeyiwa Zirin Gaza
India Ta Nutsar Da Jirgin 'Yan Fashin Jirage A Somalia
Shugaban Kwango Laurent Kabila Ya Kori Babban Hafsan Mayakan Kasar,Dakarunsa Suna Ci Gaba Da Shan Kashi A Hanun 'Yan Tawaye.
Shugabannin Kamfanonin Kera Motoci A Amurka, Zasu Bayyana A Gaban Kwamitin Majalisar Dokokin Amurka.
Babban Jirgin Ruwa Dake Dakon Mai Da Aka Sace Ya Kusa Isa Gabar Ruwan Somalia
Iraq Ta Yarda Amurka Taci Gaba Da Kasancewa Cikin Kasar Har Zuwa 2011.
'Yan Bindiga Sun Yi Fashin Wani Jirgin Dakon Kaya A Yankin Niger Deltan Najeriya
'Yan Tawaye A Kwango Sun Sake Kwace Wasu Sabbin Yankuna,A Dai Dai Lokacinda Shugabansu,Lauren Nkunda Ya Gana Da Manzon Majalisar Dinkin Duniya,Janar Obasanjo.
A Yau Litinin,Shugaban Amurka Mai Jiran Gado Barack Obama,Yana Ganawa Da Abokin Hamayyarsa A Zaben Shugaban Kasa, John McCain.
Turai Tace Kasashenda Ke Cikin Kungiyar MAsu Aiki Da Kudin Euro Suna Fuskantar Koma Bayan Tattalin Arziki
Pakistan Tana Zargin AMurka Ta Kai Hari Da Makamai Masu Linzami A Yankin Kasar.
Jam'iyyar 'Yan Hamayya MDC A Zimbabwe Tana Taron Koli Domin Tsaida Shawarar Ko Ta Shiga Gwamnatin Hada Kan Kasa
Senata Hillary Clinton Ce Obama Zai Zaba Sakatariyar Harkokin Wajen Amurka?
An Takaita Ikon Bin Laden A Alkaida
Shugaban Amurka mai Jiran Gado Barack Obama,zai Maye Gurbin Wasu Manyan Jami'an Ayyukan Lelen Asiri Biyu Cikin Watan Janairu
Majalisar Dinkin Duniya Tana Nazarin Bukatar Tura Karin Sojojin Kiyaye Zaman Lafiya A Kwango
'Yan Bindiga Sun Harbe Wani Ba Amerike  Da Matukinsa Har Lahira A Peshwar.
Sudan Ta Bada Sanarwar Tsagaita Wuta A Yankin Darfur
Shugabannin Amurka Mai Barin Gado George Bush,da Magajinsa Barack Obama, Sun Gana A Fadar White House Jiya Litinin
Hannayen Jari A Kasuwannin Turai da Asiya Sun Yi Kasa A Hada-Hadar Yinin Talata
Wata Kungiyarda Gwamnatin Sudan Ta Kafa Tana Kira Da Tsagaiata Wuta A Fafatawarda Akeyi A Yankin Darfur
Yau Ce Cikar Shekaru 90 Da Kammala Yakin Duniya Na Daya
Miriam Makeba Ta Rasu
Bam Ya Kashe Akalla Mutane Ashirin Da Takwas A Bagadaza
Shugaban Amurka Mai Barin Gado GeorgeBush ,Zai Karbi Bakuncin Shugaban Amurka Mai Jiran Gado Barack Obama A Fadar White House.
Shugabannin Siyasar Ivory Coast Sun Fara Taro Domin Tattaunawa Kan  makomar Zaben Kasar Da Ake Yawan Jinkirtawa
Shugaban Amurka Mai Jiran Gado,Barack Obama,Ya Yi Taronsa Farko Da Manema Labaru Tun Bayan Samun Nasara Zabensa
Ban Ki-moon Zai Ziyarci Kwango
Shugaban Amurka Mai Jiran Gado Ya Gana Da Masu Bashi Shawara Kan Harkokin Tattalin Arziki
Obama Ya Fara Tunkarar Tattalin Arziki
Asusun Bada Lamuni(IMF),Yace Tattalin Arzikin Kasashe Da Dama Suna Fuskantar Barazana
Ana Sa Ran Sabon Zababben Shugaban Kasar Amurka Barack Obama Zai Bayyana Sunayen Wasu Manyan Jami'an Gwamnatinsa Bada Jumawa Ba.