Maras Hoto
Search

Morgan Tsvangirai Ya Fasa Komawa Zimbabwe Asabar Din Nan

17/05/2008

Morgan Tsvangirai
Shugaban jam’iyyar hamayya ta kasar Zimbabwe ba zai koma gida kamar yadda ya shirya a yau asabar ba, a saboda dalilai na tsaro.

Wani kakakin jam’iyyar MDC ya ce sun samu bayani daga wata majiya mai tushe dangane da makarkashiyar da aka kitsa ta kashe Morgan Tsvangirai. Mr. Tsvangirai ya bar kasar Zimbabwe tun zaben shugaban kasa da na majalisar dokoki na ranar 29 ga watan Maris.

Sakamakon da hukuma ta bayar ya nuna cewa ya doke shugaba Robert Mugabe a zaben, amma bai samu fiye da rabin kuri’un da aka jefa, wanda ake bukata, don lashe zaben kai tsaye ba tare da yin zagaye na biyu ba.

Tun fari, an sa ran shugaban na jam’iyyar MDC zai koma daga kasashen Turai don fara yakin neman zaben zagaye na biyu na fitar da gwani da za a yi tsakaninsa da Mr. Mugabe ranar 27 ga watan Yuni. Jam’iyyar ta shirya wani gagarumin gangami gobe lahadi.

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin

  Muhimmin Labari
Sojoji Sun Hana Jirgin Shugaba Manuel Zelaya Na Honduras Sauka A Tegucigalpa

  Karin Labarai
A Ci Gaba Da Kokarinsa Na Yin Tazarce, Tandja Ya Rushe Kotun Tsarin Mulkin Jamhuriyar Nijar
Gwamnatin Mamadou Tandja Ta Ce Lallai Sai Ta Gudanar Da Kuri'ar Raba-Gardama
Sojoji Sun Hambarar Da Shugaban Honduras Mai Shirin Yin Tazarce
Gini Ya Rushe Ya Kashe Mutane Akalla Biyar A Lagos
Madaukakiyar Kotun Nijar Ta Soke Umurnin Da Shugaba Tandja Ya Bayar Na Shirya Zaben Raba-Gardama A Watan Agusta