Maras Hoto
Search

Morgan Tsvangirai Ya Fasa Komawa Zimbabwe Asabar Din Nan

17/05/2008

Morgan Tsvangirai
Shugaban jam’iyyar hamayya ta kasar Zimbabwe ba zai koma gida kamar yadda ya shirya a yau asabar ba, a saboda dalilai na tsaro.

Wani kakakin jam’iyyar MDC ya ce sun samu bayani daga wata majiya mai tushe dangane da makarkashiyar da aka kitsa ta kashe Morgan Tsvangirai. Mr. Tsvangirai ya bar kasar Zimbabwe tun zaben shugaban kasa da na majalisar dokoki na ranar 29 ga watan Maris.

Sakamakon da hukuma ta bayar ya nuna cewa ya doke shugaba Robert Mugabe a zaben, amma bai samu fiye da rabin kuri’un da aka jefa, wanda ake bukata, don lashe zaben kai tsaye ba tare da yin zagaye na biyu ba.

Tun fari, an sa ran shugaban na jam’iyyar MDC zai koma daga kasashen Turai don fara yakin neman zaben zagaye na biyu na fitar da gwani da za a yi tsakaninsa da Mr. Mugabe ranar 27 ga watan Yuni. Jam’iyyar ta shirya wani gagarumin gangami gobe lahadi.

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin

  Muhimmin Labari
Jami'an Sojan Iran Sun Ce An fara Wata Gagarumar Rawar Daji Ta Kare Kasa Daga Hari Ta Sama

  Karin Labarai
Yau Litinin Majalisar Dinkin Duniya Zata Kaddamar Da Aiki Mafi Girma Na Rigakafin Cutar Shawara Da Ta Taba Yi
Kwallon Kafa Ya Haddasa Rikicin Diflomasiyya Tsakanin Masar Da Aljeriya
Somaliyawa 'Yan Fashi A Teku Sun Sake Kai Hari Kan Wani Jirgin Ruwan Amurka Da Suka Taba Kamawa
Yau Alhamis Za A Rantsar Da Shugaba Hamid Karzai Na Afghanistan