Koma Ga Shafi Mai Hoto

VOANews.com
News in 44 languages


A Guinea, sojoji sun harbe wani jami’in kula da kudadensu

27/05/2008

Jami’ar rundunar sojin Guinea, sunce wadansu sojoji dake bukatar a biyasu wasu kudadensu, sun harbe wani jami’in kula da kudadens, har sun ji masa ciwo.

Jami’an sun fada a yau cewa sojojin sun raunata Manjo Korka Dioallo, a lokacin da suke wata zanga-zanga a babban birnin Guinea na Conakry. Zanga zangar ta barke ne tun a jiya Litinin, lokacin da sojojin suka rika harba harsashi a sama, a wani sansanin soji dake Conakry.

 Sojojin tsohon Prime Minista Lansana Kouyate – wanda aka kora a makon da ya gabata, yayi masu alkawarin kimanin dollar dubu daya da dari daya da suke bi bashi.

Muhimmin Labari
Jami'an Sojan Iran Sun Ce An fara Wata Gagarumar Rawar Daji Ta Kare Kasa Daga Hari Ta Sama

Karin Labarai
Yau Litinin Majalisar Dinkin Duniya Zata Kaddamar Da Aiki Mafi Girma Na Rigakafin Cutar Shawara Da Ta Taba Yi
Kwallon Kafa Ya Haddasa Rikicin Diflomasiyya Tsakanin Masar Da Aljeriya
Somaliyawa 'Yan Fashi A Teku Sun Sake Kai Hari Kan Wani Jirgin Ruwan Amurka Da Suka Taba Kamawa
Yau Alhamis Za A Rantsar Da Shugaba Hamid Karzai Na Afghanistan