A yammacin Alhamis din nan ne,ake sa ran dan takarar
shugabancin Amurka na Jam'iyyar Democrat, Barack Obama,zaiyi na'am da tsaida
shi dan takara, a jawabi da ake doki zai gabatar,wanda kuma zai kawo karshen
babban taron Jam'iyyar.
Obama
zai yi jawabi ga dubban mutane a wani dandalin wasanni mai suna "Mile High
Stadium",a birnin Denver,cikin Jihar Colorado, dake yammacin Amurka.
 |
Hillary Clinton da Barack Obama
|
Cikin
sanannun Jam'iyyar har da zasu yi
jawabi ga gangamin har da tsohon
mataimakin shugaban kasar Amurka Al Gore,da kuma Gwamnan Jihar New Mexico,Bill
Richardson, Haka kuma za a nunawa wakilai majigi kan tsohon shugaban rajin kare
hakkin bil'adama, Martin Luther King,wadda yau ce cikar shekaru 45 da gabatar
da fitaccen jawabin sa,da aka lakabawa suna "Ina Mafarki".
 |
Barack Obama da Joe Biden
|
Jiya
Laraba da dare ne taron ya tsaida Obama da mataimakin sa Joseph Biden.Obama ne
bakar fatar Amurka na farko da wata babbar Jam'iyyar siyasa ta tsayar takarar
shugabancin Amurka. A jiyan tsohon shugaban Amurka Bill Clinton, ya kira
Obama,mutumin da ya dace da aikin shugaban kasa.