Maras Hoto
Search

Ra'ayoyin Jama'a Game Da Zaben Obama

05/11/2008

Democratic presidential Barack Obama speaks about the economy in the Great Hall at Cooper Union in New York, 27 Mar 2008
Barack Obama
Ojo na titin Bugaje (titinbougajeojo@yahoo.fr) BP : 486 Zinder a Jamhuriyar Nijar, ya rubuto yana cewa, "...sashen hausa na muryar amurka ku gayama shuwagabannin siyasa  na kasarmu  Niger, Zaben kasar Amurka ya kamata ya zame musu ishara, saboda sunga yinda dan adawa zai fadi a takarar neman kuri'a ta zabe, kuma ya amince da lalle ya fadi, sannan ya kirayi magoya bayenshi da su mara ma wanda yaci domin a tafi tare dan ama kasa aiki, a gaskia wannan abu sai a Amurka. Allah yasa shuwagabanninmu wannan ishara zata zamo musu karatu a kayunansu, amin."

IBRAHIM JATAU MAI NAMA BISIJE MALUMFASHI, tare da YUSUF MAIKANO LUNGUN ALHAZAWA MALUMFASHI, sun rubuto su na cewa, "Barak Obama yau an wayi gari ALLAH yasa ka zama shugaban kasar Amurka, saura ka cika alkawuran duk da ka dauka, ka kuma yi kokarin dawo da martabar AMURKA A IDANUN DUNIYA."

Democratic presidential candidate Sen. Barack Obama speaks during a rally in Jacksonville, Florida, 3 Nov. 2008
Barack Obama
"Hakika  Amirkawa tabbas kunzama zakarar gwajin dafin duniya, ga shi kunyi zabenku lafiya cike da adalci, da sanin yakamata, to, Obama sai ka rike kowa hannu biyu biyu, sannan kada kamanta da irin goyon bayan da 'yan uwanka al'umar Afirka suka baka. To, yaya  babbar kwabo wato Najeriya  kinga yanda ake tafiyar da zabe cikin adalci, ba 'yan banga. ba fisge akwatun zabe, babu aiki da 'yan sanda dan su musguna ma masu kada kuri'a, to, yaya babbar kwabo Najeriya  sai kigyara tsarin zabenki  indai  kina son kici gaba da hura hanci a kasashen Afirika." Daga Sani World 7 Kusfa Zaria.(Saniworld7kusfazaria@yahoo.com)

SHUAIBU MUHAMMED RIJIYAR MAIKABI(RKB20042001@YAHOO.COM)ya rubuto ta sa takardar yana fadin cewa, "Ra'ayina shine In nuna farin cikina kan yadda "yan kasar Amuruka suka debewa kansu takaici suka tsaya suka nuna su na da "yanci sannan inyi kira ga sabon Shugaban kasar ta Amuruka wato Barack Obama da ya cika Alkawalinda yadauka yatsaya tsayin daka don maido wa kasar Amuruka martabarta."

Muhammed Usman Dandattijo Bayan NEPA, Malumfashi, Jihar Katsina, ya ce, "Assalamu alaikum ina taya Barack Obama da sauran al'umar Afrika dama duniya baki daya murnar samun nasarar cin zaben dan'uwanmu Barack Obama. Allah Ya yi masa jagora da fatan zai ba marada kunya."

emailme.gif Aika da Wannan sako ta E-Mail
printerfriendly.gif Buga Wannan Shafin

  Muhimmin Labari
Shugaba Barack Obama Ya Fara Ziyararsa Ta Farko A Nahiyar Asiya

  Karin Labarai
Daga Mai Neman Koyan Hausa Na Zamo Babbar Mai Sha'awar Fina-Finai Da Wakokin Hausa  Audio Clip Available
ECOWAS Ta Ce Ba Zata Amince Da Sakamakon Zaben Da Aka Yi A Nijar Ba
Yau Talata Kungiyar ECOWAS Za Ta Bayyana Dakatar Da Jamhuriyar Nijar Daga Cikin Kungiyar
Shugabannin Afirka Ta Yamma Zasu Yi Taron Koli Kan Guinea-Conakry