VOANews.com

 

Yau A VOA:

Labarai Cikin Harsuna 45
Nijar Ta Mika Kuka Ga Hukumomin Nijeriya Kan Kagen Da Ta Ce An Yi Ma 'Yan Kasarta A Jos

04/12/2008

Shugaba Mamadou Tandja na Nijar
Shugaba Mamadou Tandja na Nijar
Nijar ta mika takardar kuka ga hukumomin makwabciyarta Nijeriya dangane da kagen da ta ce an yi mata kan ta kyale 'yan kasarta sojojin haya sun shiga cikin mummunan fadan addini.

A ranar talata ce gwamnatin Jihar Filato ta ce ta kama wasu 'yan Nijar su 16 a bayan da aka kashe daruruwan mutane a rikicin addini a garin Jos. Hukumomin na Jihar Filato sun yi zargin cewa wadannan 'yan Nijar sun yi tattaki zuwa Jos din ne da nufin gwabza fadan addini.

Sai dai ma'aikatar harkokin wajen Nijar ta fada yau alhamis cewar ta mika takardar kuka da babbar murya ga Nijeriya, inda balo-balo ta karyata wannan zargin da ta ce ba ya da wata madafa. Ma'aikatar ta fada cikin wata sanarwa cewa mutanen da aka kama, mutane ne da suka yi shekara da shekaru su na zaune a Jos su na yin sana'a a can.

Sanarwar ta ce an tura jakadan Nijar a Nijeriya, Isa Ibrahim, zuwa Jos domin ya ganewa idanunsa yadda al'amura suke a can.

 


E-mail This Article Aika Labarin Nan ma Wani Ta E-Mail
Print This Article Shafi Mai Saukin Bugawa
  Muhimmin Labari
Daga Mai Neman Koyan Hausa Na Zamo Babbar Mai Sha'awar Fina-Finai Da Wakokin Hausa  Audio Clip Available

  Karin Labarai
ECOWAS Ta Ce Ba Zata Amince Da Sakamakon Zaben Da Aka Yi A Nijar Ba
Yau Talata Kungiyar ECOWAS Za Ta Bayyana Dakatar Da Jamhuriyar Nijar Daga Cikin Kungiyar
Shugabannin Afirka Ta Yamma Zasu Yi Taron Koli Kan Guinea-Conakry
Ghana Ta Kai Wasan Karshe Na Cin Kofin Kwallon Kafar Duniya Na Matasa A Masar