VOANews.com

 

Yau A VOA:

Labarai Cikin Harsuna 45
Nijar Ta Mika Kuka Ga Hukumomin Nijeriya Kan Kagen Da Ta Ce An Yi Ma 'Yan Kasarta A Jos

04/12/2008

Shugaba Mamadou Tandja na Nijar
Shugaba Mamadou Tandja na Nijar
Nijar ta mika takardar kuka ga hukumomin makwabciyarta Nijeriya dangane da kagen da ta ce an yi mata kan ta kyale 'yan kasarta sojojin haya sun shiga cikin mummunan fadan addini.

A ranar talata ce gwamnatin Jihar Filato ta ce ta kama wasu 'yan Nijar su 16 a bayan da aka kashe daruruwan mutane a rikicin addini a garin Jos. Hukumomin na Jihar Filato sun yi zargin cewa wadannan 'yan Nijar sun yi tattaki zuwa Jos din ne da nufin gwabza fadan addini.

Sai dai ma'aikatar harkokin wajen Nijar ta fada yau alhamis cewar ta mika takardar kuka da babbar murya ga Nijeriya, inda balo-balo ta karyata wannan zargin da ta ce ba ya da wata madafa. Ma'aikatar ta fada cikin wata sanarwa cewa mutanen da aka kama, mutane ne da suka yi shekara da shekaru su na zaune a Jos su na yin sana'a a can.

Sanarwar ta ce an tura jakadan Nijar a Nijeriya, Isa Ibrahim, zuwa Jos domin ya ganewa idanunsa yadda al'amura suke a can.

 


E-mail This Article Aika Labarin Nan ma Wani Ta E-Mail
Print This Article Shafi Mai Saukin Bugawa
  Muhimmin Labari
Yau Miliyoyin Musulmi Mahajjata Suke Hawan Arafat, Yayin Da Ruwan Sama Ya Kashe Mutane 11

  Karin Labarai
Yau Fiye Da Wata Shida Ba A Biya Sojojin Kiyaye Zaman Lafiya Dake Somaliya Albashinsu Ba
Shugaba Barack Obama Zai Bayyana Sabuwar Manufarsa Kan Afghanistan A Ranar Talata
Jami'an Sojan Iran Sun Ce An fara Wata Gagarumar Rawar Daji Ta Kare Kasa Daga Hari Ta Sama
Yau Litinin Majalisar Dinkin Duniya Zata Kaddamar Da Aiki Mafi Girma Na Rigakafin Cutar Shawara Da Ta Taba Yi