VOANews.com

 
Labarai Cikin Harsuna 45
Sashen Hausa Na Muryar Amurka Yana Bukukuwan Cika Shekaru 30

26/01/2009

Ma'aikatan Sashen Hausa
Ma'aikatan Sashen Hausa
A cikin wannan makon ne Sashen hausa na Muryar Amurka yake kaddamar da bukukuwan cikar shekaru 30 da kafuwa. Sashen ya fara gabatar da shirye-shiryen Hausa a ranar 21 ga watan Janairun 1979, amma a saboda bukuwan rantsar da sabon shugaban Amurka da aka yi a makon, sai aka dage zuwa wannan makon da muke ciki.

A cikin wata sanarwar da ya bayar a nan Washington, shugaban Sashen Hausa, Sunday Dare, ya ce uwargidan shugaban Nijeriya, Hajiya Turai 'Yar'aduwa, ita ce zata jagoranci babban bukin da za a gudanar a ranar alhamis, 29 ga watan Janairu.

Wadanda zasu tallafa mata wajen jagorancin wannan bukin, sun hada har da gwamnonin jihohin Sakkwato, Kebbi, Yobe da kuma Filato. Tuni har wasu daga cikin bakin da za su halarci wannan buki sun iso nan birnin Washington.

A bangaren shirye-shirye kuma, tun daga shirin safiyar talata za a fara gabatar da wasu shirye-shirye masu nasaba da tarihin kafa wannan Sashe, da kuma yadda ya taso har ya zuwa wannan matsayin da ake daukarsa a zaman daya daga cikin mafiya tasiri a duniya.

Za a bada masu sauraro damar su bayyana ra'ayoyinsu a kan Sashen Hausa na Muryar Amurka a cikin shirye-shirye na musamman da za a yi ta gabatarwa a duk tsawon wannan makon.


E-mail This Article Aika Labarin Nan ma Wani Ta E-Mail
Print This Article Shafi Mai Saukin Bugawa
  Muhimmin Labari
Kwallon Kafa Ya Haddasa Rikicin Diflomasiyya Tsakanin Masar Da Aljeriya

  Karin Labarai
Somaliyawa 'Yan Fashi A Teku Sun Sake Kai Hari Kan Wani Jirgin Ruwan Amurka Da Suka Taba Kamawa
Yau Alhamis Za A Rantsar Da Shugaba Hamid Karzai Na Afghanistan
Switzerland Ta Doke Nijeriya A Wasan Karshe Na Cin Kofin Kwallon Kafar Duniya Na Samari
Dan Kunar-Bakin-Wake Ya Kai Farmaki Kan Hukumar Leken Asirin Pakistan