VOANews.com

 
Labarai Cikin Harsuna 45
Wasu 'Yan Rasha Biyu Da Ake Garkuwa Da Su A Niger-Delta Sun Tsere Ma 'Yan Tsageru

20/02/2009

Nigerian separatist rebel brandishes his weapon in a show of strength for reporters <br/> (File photo)
'Yan tsageran Niger Delta
Rundunar sojojin Nijeriya ta ce wasu 'yan kasar Rasha su biyu da aka sace watanni biyu da suka shige, sun tsere daga hannun mutanen da suke yin garkuwa da su, kuma an ceto su.

Wani kakakin sojojin, Kanar Sagir Musa, ya ce mutanen biyu sun tsere da kafa daga sansanin da ake yin garkuwa da su. Sun shafe kwanaki biyar su na yawo a cikin fadamu na yankin Niger Delta. Jiya alhamis wasu sojojin Nijeriya dake yin sintiri a yankin suka tsince su, suka fito da su waje. 

'Yan kasar ta Rasha su na yin aiki ne a wata masana'antar goran ruwa dake garin Ikot Abasi mai tashar jiragen ruwa a Jihar Akwa Ibom.

Sace mutane da kai hare-hare sun zamo ruwan dare a yankin kudancin Nijeriya mai arzikin fetur. Har yanzu Nijeriya ce kasar da ta fi sayarwa da kasashen waje man fetur a nahiyar Afirka duk da cewa yawan man da take hakowa ya ragu da kashi ashirin cikin 100 a shekaru ukun da suka shige a saboda sace-sacen mutane da hare-haren da ake kaiwa kan cibiyoyin mai na yankin.


E-mail This Article Aika Labarin Nan ma Wani Ta E-Mail
Print This Article Shafi Mai Saukin Bugawa
  Muhimmin Labari
Jami'an Sojan Iran Sun Ce An fara Wata Gagarumar Rawar Daji Ta Kare Kasa Daga Hari Ta Sama

  Karin Labarai
Yau Litinin Majalisar Dinkin Duniya Zata Kaddamar Da Aiki Mafi Girma Na Rigakafin Cutar Shawara Da Ta Taba Yi
Kwallon Kafa Ya Haddasa Rikicin Diflomasiyya Tsakanin Masar Da Aljeriya
Somaliyawa 'Yan Fashi A Teku Sun Sake Kai Hari Kan Wani Jirgin Ruwan Amurka Da Suka Taba Kamawa
Yau Alhamis Za A Rantsar Da Shugaba Hamid Karzai Na Afghanistan