VOANews.com

 
Labarai Cikin Harsuna 45
An Sako 'Yar Kasar Canada Da Aka Sace A Kaduna

30/04/2009

Umaru Yar'Adua
Shugaban Nijeriya, Umaru Yar'Adua
An sako wata mace 'yar kasar Canada da aka sace a farkon wannan wata a Nijeriya, an kuma mika ta ga jami'an kasar Canada.

Wani kakakin ma'aikatar harkokin wajen Canada ya fada a birnin Ottawa cewa a yanzu Julie Mulligan "tana nan lafiyarta kalau, kuma tana hannun jami'an Canada." A cikin wata sanarwar da ya bayar larabar nan, kakakin ya ce ana kyautata zaton nan ba da jimawa ba Mulligan zata yi ido hudu da iyalanta.

A ranar 16 ga watan Afrilu wasu 'yan bindiga suka sace Mulligan a birnin Kaduna dake arewacin Nijeriya. Kwanaki da dama a bayan wannan, mutanen ad suka sace ta sun yi ikirarin cewa ba ta da lafiya sosai, tana fama da zazzabin cizon sauro da kuma kuraje.

Da farko, 'yan sandan Nijeriya sun ce mutanen da suka sace Mulligan sun nemi da a biya su kudin fansa. Amma kuma ba a ji labarin ko an biya su kudin fansar ba.

Sace mutane ad wasu hare-hare sun zamo ruwan dare a yankin Niger Delta na kudancin Nijeriya, amma ba a saba ganin irin wannan a sauran sassan Nijeriya ba.


E-mail This Article Aika Labarin Nan ma Wani Ta E-Mail
Print This Article Shafi Mai Saukin Bugawa
  Muhimmin Labari
Jami'an Sojan Iran Sun Ce An fara Wata Gagarumar Rawar Daji Ta Kare Kasa Daga Hari Ta Sama

  Karin Labarai
Yau Litinin Majalisar Dinkin Duniya Zata Kaddamar Da Aiki Mafi Girma Na Rigakafin Cutar Shawara Da Ta Taba Yi
Kwallon Kafa Ya Haddasa Rikicin Diflomasiyya Tsakanin Masar Da Aljeriya
Somaliyawa 'Yan Fashi A Teku Sun Sake Kai Hari Kan Wani Jirgin Ruwan Amurka Da Suka Taba Kamawa
Yau Alhamis Za A Rantsar Da Shugaba Hamid Karzai Na Afghanistan