VOANews.com

 
Labarai Cikin Harsuna 45
An Gurfanar Da Nasiru el-Rufa'i A Gaban Kotu

07/05/2009

Umaru Yar'Adua in Abuja
Umaru Yar'Adua
An sake gurfanar da wani tsohon minista na tsohuwar gwamnatin Olusegun Obasanjo a gaban kotu a Nijeriya. 

A jiya Laraba Hukumar Yaki da Laifuffukan Tattalin Arziki ta EFCC ta tuhumi Malam Nasir El Rufa'i, tsohon ministan babban birnin tarayya, Abuja, da laifuffuka takwas na hadin baki, da rashawa.

Masu bincike sun zargi Malam El Rufa'i da laifin yin amfani da matsayinsa, ya bayar da wani fili na Hukumar Samar da Wutar Lantarki, wanda ya saba wa dokokin kasa.

Ance Ministan Babban Birnin Taraiya na yanzu, ya fara soke takardun mallakar wasu filaye da Malam El Rufa'i ya bayar a karshen wa'adin aikinsa.

Shugaba Obasanjo dai yana shan zarge zargen rashawa, tare da wasu daga cikin manyan jami'an gwamnatin sa.


E-mail This Article Aika Labarin Nan ma Wani Ta E-Mail
Print This Article Shafi Mai Saukin Bugawa
  Muhimmin Labari
Jami'an Sojan Iran Sun Ce An fara Wata Gagarumar Rawar Daji Ta Kare Kasa Daga Hari Ta Sama

  Karin Labarai
Yau Litinin Majalisar Dinkin Duniya Zata Kaddamar Da Aiki Mafi Girma Na Rigakafin Cutar Shawara Da Ta Taba Yi
Kwallon Kafa Ya Haddasa Rikicin Diflomasiyya Tsakanin Masar Da Aljeriya
Somaliyawa 'Yan Fashi A Teku Sun Sake Kai Hari Kan Wani Jirgin Ruwan Amurka Da Suka Taba Kamawa
Yau Alhamis Za A Rantsar Da Shugaba Hamid Karzai Na Afghanistan