VOANews.com

 
Labarai Cikin Harsuna 45
Kamfanin Man Shell Zai Biya Diyyar Dala Miliyan Goma Sha Biyar Ga Wasu 'Yan Nijeriya

09/06/2009

Shell
Shell
Kamfanin man fetur na Shell      ya yarda zai biya dala miliyan 15 da dubu dari biyar ga wadanda suka kai      kararsa bisa zargin hannu a keta hakkin bil Adama a Nijeriya, domin su      janye wannan karar.

Wannan yarjejeniyar biyan kudin da aka cimma jiya      litinin a New York ita ta kawo karshen shari’ar da aka shafe shekaru fiye      da gom ana gwabzawa a tsakanin kamfanin Shell da ‘yan’uwan masu      zanga-zangar da tsohuwar gwamnatin mulkin soja ta Nijeriya ta yankewa      hukumcin kisa a 1995.

Mutanen sun hada da marubucin wakoki Ken Saro-Wiwa,      wanda ya jagoranci zanga-zangar rashin amincewa da zaman kamfanin Shell a      yankin Niger Delta. Masu zanga-zangar sun ce kamfanin Shell ya gurbata      yanayin yankin ya kuma keta hakkin ‘yan kabilar Ogoni.

Haka kuma sun zargi      kamfanin da laifin hada baki da gwamnati wajen hukumta wadanda suka soki      lamirin kamfanin. Kamfanin Shell dai ya ce shi bai aikata wani laifi ba,      amma yace ya yarda mutanen sun sha wahala. 


E-mail This Article Aika Labarin Nan ma Wani Ta E-Mail
Print This Article Shafi Mai Saukin Bugawa
  Muhimmin Labari
An Sako Faransawan Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Darfur

  Karin Labarai
White House Ta Ce Isra'ila Tana Gurgunta Kokarin Samar Da Zaman Lafiya
NAHIYAR AFIRKA TA YI TARON DANGI DON YAKI DA BARKEWAR CUTAR POLIO
Taliban Ta dauki Alhakin Hare Hare Da Ya Kashe Akalla Mutane Talatin a Kandahar
Gungun Kasashe Masu Shiga Tsakani A rikicin Gabas Ta Tsakiya Sun Yi Allah Wadai Da Isra'ila
Alakar Jinyar Tarin Fuka, TB, Da Kanjamau Ko SIDA
Zirga Zirga Tsakanin Arewa Da Kudancin Najeriya Ta Tsaya Cik Ranar Jummaa
Didier Drogba Shi Ne Zakaran Kwallon Kafa Na Afirka Na 2009