Madaukakiyar Kotun Nijar Ta Soke Umurnin Da Shugaba Tandja Ya Bayar Na Shirya Zaben Raba-Gardama A Watan Agusta
Marubuci Ibrahim Alfa Ahmed 13/06/2009
Shugaba Mamadou Tandja na Nijar
Madaukakiyar
kotun Jamhuriyar Nijar ta yanke hukumcin cewa shirin shugaba Mamadou Tandja na
gudanar da kuri'ar raba-gardama domin kara tsawon wa'adinsa a kan mulki ya saba
ma doka, saboda haka haramun ne.
Jiya jumma'a kotun tsarin mulki ta Jamhuriyar
Nijar ta ce ta soke umurnin da shugaba Tandja ya bayar ranar 5 ga watan Yuni a kan a gudanar da kuri'ar raba-gardamar a cikin watan Agusta.
Kotun ta ce umurnin da
shugaban ya bayar ya saba ma tsarin mulkin Jamhuriyar Nijar. Tsarin mulkin ya
kayyade cewa shugaban kasa zai iya yin wa'adi biyu ne kawai na shekaru
biyar-biyar a jere kan mulki.
Shugaba Tandja ya ce yana son karin lokaci a kan
kujerar shugaban kasar domin ya kashe wutar tawayen da Abzinawa suke yi, da
fadada ayyukan samar da kayan bukatu da kuma ba da karin iko ga kujerar
shugaban kasa.
Wannan shiri nasa ya hassala 'yan hamayyar siyasa da shugabannin
kwadago na Jamhuriyar Nijar. Haka kuma, hukumomin kasashen Afirka da kuma
gwamnatin Amurka sun fito da kakkausar harshe su na sukar lamirin wannan shirin
yin Tazarce.
Wa'adin shugaba Tandja a kan mulki zai kare a watan Disamba, amma
ya sha nanata cewa ya kamata a canja wannan.
A can baya, kotun tsarin mulkin ta
ayyana cewa shirin Tazarcen na shugaba Tandja ya keta doka. A bayan wannan ne
sai shugaban ya rushe majalisar dokoki. Sai dai kuma hukumcin da Kotun Tsarin
Mulkin ta yanke a jiya jumma'a, hukumci
ne da tsarin mulkin kasar ya bukaci cewa tilas a yi aiki da shi.