VOANews.com

 
Labarai Cikin Harsuna 45
Gini Ya Rushe Ya Kashe Mutane Akalla Biyar A Lagos

29/06/2009

[insert caption here]
Wata mace na kuka a inda gini ya rushe a Lagos
Hukumomin Nijeriya sun ce mutane akalla biyar sun mutu a lokacin da wani gini mai hawa uku ya rushe a Lagos, cibiyar kasuwancin kasar. An ceto wasu mutanen su akalla talatin.

Masu aikin ceto sun ce haka kwatsam wannan gini ya rushe ranar lahadi. Babu wani bayanin da aka samu a game da dalilin rushewar wannan bene.

A watan Maris, mutane akalla 11 sun mutu a lokacin da wani benen mai hawa hudu shi ma ya rushe a birnin na Lagos.

Rushewar gine-gine dai ba sabon abu ba ne a Nijeriya, inda magina suke yin ko oho da ka'idojin yin gini da gwamnati ke shimfidawa, suke kuma yin amfani da kayayyakin ginin da ba su dace ba, ko kuma ba su da aminci.


E-mail This Article Aika Labarin Nan ma Wani Ta E-Mail
Print This Article Shafi Mai Saukin Bugawa
  Muhimmin Labari
Daga Mai Neman Koyan Hausa Na Zamo Babbar Mai Sha'awar Fina-Finai Da Wakokin Hausa  Audio Clip Available

  Karin Labarai
ECOWAS Ta Ce Ba Zata Amince Da Sakamakon Zaben Da Aka Yi A Nijar Ba
Yau Talata Kungiyar ECOWAS Za Ta Bayyana Dakatar Da Jamhuriyar Nijar Daga Cikin Kungiyar
Shugabannin Afirka Ta Yamma Zasu Yi Taron Koli Kan Guinea-Conakry
Ghana Ta Kai Wasan Karshe Na Cin Kofin Kwallon Kafar Duniya Na Matasa A Masar