VOANews.com

 
Labarai Cikin Harsuna 45
Gini Ya Rushe Ya Kashe Mutane Akalla Biyar A Lagos

29/06/2009

[insert caption here]
Wata mace na kuka a inda gini ya rushe a Lagos
Hukumomin Nijeriya sun ce mutane akalla biyar sun mutu a lokacin da wani gini mai hawa uku ya rushe a Lagos, cibiyar kasuwancin kasar. An ceto wasu mutanen su akalla talatin.

Masu aikin ceto sun ce haka kwatsam wannan gini ya rushe ranar lahadi. Babu wani bayanin da aka samu a game da dalilin rushewar wannan bene.

A watan Maris, mutane akalla 11 sun mutu a lokacin da wani benen mai hawa hudu shi ma ya rushe a birnin na Lagos.

Rushewar gine-gine dai ba sabon abu ba ne a Nijeriya, inda magina suke yin ko oho da ka'idojin yin gini da gwamnati ke shimfidawa, suke kuma yin amfani da kayayyakin ginin da ba su dace ba, ko kuma ba su da aminci.


E-mail This Article Aika Labarin Nan ma Wani Ta E-Mail
Print This Article Shafi Mai Saukin Bugawa
  Muhimmin Labari
Yau Miliyoyin Musulmi Mahajjata Suke Hawan Arafat, Yayin Da Ruwan Sama Ya Kashe Mutane 11

  Karin Labarai
Yau Fiye Da Wata Shida Ba A Biya Sojojin Kiyaye Zaman Lafiya Dake Somaliya Albashinsu Ba
Shugaba Barack Obama Zai Bayyana Sabuwar Manufarsa Kan Afghanistan A Ranar Talata
Jami'an Sojan Iran Sun Ce An fara Wata Gagarumar Rawar Daji Ta Kare Kasa Daga Hari Ta Sama
Yau Litinin Majalisar Dinkin Duniya Zata Kaddamar Da Aiki Mafi Girma Na Rigakafin Cutar Shawara Da Ta Taba Yi