 |
| Shugaba Mamadou Tandja na Nijar |
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta ce za a gudanar da kuri'ar raba-gardamar da zata iya ba shugaba Mamadou Tandja damar yin tazarce, duk da cewa kotu ta haramta yin hakan, 'yan hamayya kuma sun nuna rashin yardarsu.A lokacin da yake magana lahadi, ministan harkokin cikin gidan Nijar, Albade Abouba, ya ce lallai za a gudanar da wannan kuri'ar raba-gardama, har ma ya nuna yatsar yin barazana ga 'yan hamayya dake kushe shugaba Tandja.
A ranar jumma'a shugaba Tandja ya ce daga yanzu zai rungumi ragamar mulki a kasar shi kadai, a bayan da Kotun Tsarin Mulki ta Jamhuriyar Nijar ta jaddada hukumcin da ya haramta gudanar da kuri'ar raba-gardama domin sauya tsarin mulki.
A ranar asabar, 'yan hamayya na Nijar sun bayyana matakan da shugaba Tandja ya dauka a matsayin juyin mulki, sun kuma yi kira ga dakarun tsaron kasar da su ki bin umurnin da shugaban zai ba su.
Shugaba Tandja da 'yan kanzagin Tazarce su na son a gudanar da kuri'ar raba-gardamar a ranar 4 ga watan Agusta.