VOANews.com

 
Labarai Cikin Harsuna 45
Gwamnatin Mamadou Tandja Ta Ce Lallai Sai Ta Gudanar Da Kuri'ar Raba-Gardama

29/06/2009

Shugaba Mamadou Tandja na Nijar
Shugaba Mamadou Tandja na Nijar
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta ce za a gudanar da kuri'ar raba-gardamar da zata iya ba shugaba Mamadou Tandja damar yin tazarce, duk da cewa kotu ta haramta yin hakan, 'yan hamayya kuma sun nuna rashin yardarsu.

A lokacin da yake magana lahadi, ministan harkokin cikin gidan Nijar, Albade Abouba, ya ce lallai za a gudanar da wannan kuri'ar raba-gardama, har ma ya nuna yatsar yin barazana ga 'yan hamayya dake kushe shugaba Tandja.

A ranar jumma'a shugaba Tandja ya ce daga yanzu zai rungumi ragamar mulki a kasar shi kadai, a bayan da Kotun Tsarin Mulki ta Jamhuriyar Nijar ta jaddada hukumcin da ya haramta gudanar da kuri'ar raba-gardama domin sauya tsarin mulki.

A ranar asabar, 'yan hamayya na Nijar sun bayyana matakan da shugaba Tandja ya dauka a matsayin juyin mulki, sun kuma yi kira ga dakarun tsaron kasar da su ki bin umurnin da shugaban zai ba su.

Shugaba Tandja da 'yan kanzagin Tazarce su na son a gudanar da kuri'ar raba-gardamar a ranar 4 ga watan Agusta.


E-mail This Article Aika Labarin Nan ma Wani Ta E-Mail
Print This Article Shafi Mai Saukin Bugawa
  Muhimmin Labari
Jami'an Sojan Iran Sun Ce An fara Wata Gagarumar Rawar Daji Ta Kare Kasa Daga Hari Ta Sama

  Karin Labarai
Yau Litinin Majalisar Dinkin Duniya Zata Kaddamar Da Aiki Mafi Girma Na Rigakafin Cutar Shawara Da Ta Taba Yi
Kwallon Kafa Ya Haddasa Rikicin Diflomasiyya Tsakanin Masar Da Aljeriya
Somaliyawa 'Yan Fashi A Teku Sun Sake Kai Hari Kan Wani Jirgin Ruwan Amurka Da Suka Taba Kamawa
Yau Alhamis Za A Rantsar Da Shugaba Hamid Karzai Na Afghanistan