VOANews.com

 
Labarai Cikin Harsuna 45
Asabar Din Nan Musulmin Duniya Zasu Fara Azumin Watan Ramadan

21/08/2009

[insert caption here]
Musulmi Su Na sallah
Akasarin al'ummar Musulmi a fadin duniya su na shirye-shiryen fara azumin watan Ramadan, wata mai tsarki a Musulunci, daga asabar. Addinin Musulunci yana amfani da bayyanar wata wajen tsaida ranar farko ko ta karshen wata.

Shugabannin addinin Musulunci a fadin duniya sun ce ba a samu ganin wata ba a ranar alhamis, a saboda haka aka tsaida jumma'a ta zamo ranar karshe ta watan Sha'aban.

Musulmi a kasashe kamar Nijeriya, Aljeriya, masar, Indonesiya, Iraqi, Sudan, Syria, Somaliya, kasashen yankin Gulf da yankunan Falasdinawa da ma nan Amurka duk zasu tashi da azumi asabar idan Allah Ya kai mu.

A tsawon watan Ramadan, Musulmi su na gujewa cin abinci ko shan ruwa ko jima'i da wasu abubuwan da dama daga ketowar alfijir har zuwa faduwar rana.


E-mail This Article Aika Labarin Nan ma Wani Ta E-Mail
Print This Article Shafi Mai Saukin Bugawa
  Muhimmin Labari
Yau Ce Ranar Badar A Majalisar Wakilan Amurka Kan Dokar Grambawul Ga Tsarin Inshoran Kiwon Lafiya A Amurka

  Karin Labarai
Nahiyar Afirka ta yi taron dangi don yaki da barkewar cutar Polio
    Fiya da mutane miliyan 9 ne ke kamuwa da cutar tarin fuka (TB) duk    shekara, inda miliyan 1.7 daga cikinsu kan mutu 
Nijeriya Ta Janye Jakadanta Daga Libya
Goodluck Jonathan Ya Saukar Da Dukkan Ministoci
An Yi Sabon Rikici A Jihar Filato
Aljeriya Ta Cimma Yarjejeniya Da Wasu Kasashen Afirka Shida Wajen Yaki Da Taaddanci