VOANews.com

 
Labarai Cikin Harsuna 45
Shirin Ahuwa Ga Tsageran Niger-Delta Yana Tafiyar Hawainiya A Nijeriya

21/08/2009

Masked Ateke Tom militants hold their guns as they arrive at their camp (File)
Tsagera na Kungiyar Ateke Tom
Da alamun shirin da gwamnatin Nijeriya ta bullo da shi na yin ahuwa ga ‘yan tsagera a yankin Niger Delta mai arzikin man fetutr yana tafiyar hawainiya.

Tun lokacin da aka fara aiwatar da shirin na kwanaki 60 makonni biyu da suka shige, daruruwan ‘yan tsagera sun mika makamansu. Wannan adadin kuwa, kalilan ne daga kiyasin cewa yawan ‘yan tsagera dake dauke da makamai zai kai dubu 10.

An ce da yawa daga cikin ‘yan tsageran su na dari-darin mika makamansu saboda fargabar cewa gwamnati ba zata cika alkawarinta na yin ahuwar ba. Jami’an Nijeriya su na fata tsagera masu yawa zasu mika makamansu a karshen makon nan.

A watan Yuni shugaba Umaru Musa 'Yar'aduwa na Nijeriya yayi tayin ahuwa ga tsageran da suka daina kai hari kan cibiyoyin mai suka ajiye makamansu nan da ranar 4 ga watan Oktoba.


E-mail This Article Aika Labarin Nan ma Wani Ta E-Mail
Print This Article Shafi Mai Saukin Bugawa
  Muhimmin Labari
Kwallon Kafa Ya Haddasa Rikicin Diflomasiyya Tsakanin Masar Da Aljeriya

  Karin Labarai
Somaliyawa 'Yan Fashi A Teku Sun Sake Kai Hari Kan Wani Jirgin Ruwan Amurka Da Suka Taba Kamawa
Yau Alhamis Za A Rantsar Da Shugaba Hamid Karzai Na Afghanistan
Switzerland Ta Doke Nijeriya A Wasan Karshe Na Cin Kofin Kwallon Kafar Duniya Na Samari
Dan Kunar-Bakin-Wake Ya Kai Farmaki Kan Hukumar Leken Asirin Pakistan