Shirin Ahuwa Ga Tsageran Niger-Delta Yana Tafiyar Hawainiya A Nijeriya
Marubuci Ibrahim Alfa Ahmed 21/08/2009
Tsagera na Kungiyar Ateke Tom
Da
alamun shirin da gwamnatin Nijeriya ta bullo da shi na yin ahuwa ga ‘yan tsagera
a yankin Niger Delta mai arzikin man fetutr yana tafiyar hawainiya.
Tun lokacin
da aka fara aiwatar da shirin na kwanaki 60 makonni biyu da suka shige,
daruruwan ‘yan tsagera sun mika makamansu. Wannan adadin kuwa, kalilan ne daga
kiyasin cewa yawan ‘yan tsagera dake dauke da makamai zai kai dubu 10.
An ce da
yawa daga cikin ‘yan tsageran su na dari-darin mika makamansu saboda fargabar
cewa gwamnati ba zata cika alkawarinta na yin ahuwar ba. Jami’an Nijeriya su na
fata tsagera masu yawa zasu mika makamansu a karshen makon nan.
A watan Yuni
shugaba Umaru Musa 'Yar'aduwa na Nijeriya yayi tayin ahuwa ga tsageran da suka
daina kai hari kan cibiyoyin mai suka ajiye makamansu nan da ranar 4 ga watan
Oktoba.