VOANews.com

 
Labarai Cikin Harsuna 45
Tsageran Niger Delta Zasu Ci Gaba Da Aiki Da Shirin Tsagaita Wuta

16/09/2009

Madugun Tsageran Niger Delta, Ateke Tom, tare da Ibrahim Alfa Ahmed
Madugun Tsageran Niger Delta, Ateke Tom, tare da Ibrahim Alfa Ahmed
‘Yan tsagera a yankin Niger Delta mai arzikin man fetur a kudancin Nijeriya, sun ce zasu ci gaba da yin aiki da shirin tsagaita wuta na karin wata daya nan gaba, amma sun gargadi gwamnati cewa har yanzu shirinta na yin ahuwa bai takali muhimman batutuwan dake addabarsu ba.

Kungiyar MEND ta ce zata sabunta  tsagaita wutar da aka yi watanni biyu ana aiki da ita, wadda wa’adinta ya cika da karfe 12 na daren talata.

Amma kungiyar ta ce ahuwar da shugaba Umaru Musa ‘Yar’aduwa yayi tayi, ba ta tanadi yin tattaunawa mai ma’ana a kan musabbabin rikicin yankin na Niger Delta ba. Kungiyar ta yi barazanar kai sabbin hare-hare a kan cibiyoyin mai idan har ba a gudanar da tattaunawa mai ma’ana ba.

Kungiyar MEND ba ta yi ikirarin daukar alhakin ko da hari guda daya ba tun bayan da ta ayyana tsagaita wutar a ranar 15 ga watan Yuli.

Shugaba ‘Yar’aduwa yana tayin ahuwa ga dukkan ‘yan tsageran Niger Delta da suka mika makamansu suka kuma tsame hannu daga tashin hankali.

E-mail This Article Aika Labarin Nan ma Wani Ta E-Mail
Print This Article Shafi Mai Saukin Bugawa
  Muhimmin Labari
Jami'an Sojan Iran Sun Ce An fara Wata Gagarumar Rawar Daji Ta Kare Kasa Daga Hari Ta Sama

  Karin Labarai
Yau Litinin Majalisar Dinkin Duniya Zata Kaddamar Da Aiki Mafi Girma Na Rigakafin Cutar Shawara Da Ta Taba Yi
Kwallon Kafa Ya Haddasa Rikicin Diflomasiyya Tsakanin Masar Da Aljeriya
Somaliyawa 'Yan Fashi A Teku Sun Sake Kai Hari Kan Wani Jirgin Ruwan Amurka Da Suka Taba Kamawa
Yau Alhamis Za A Rantsar Da Shugaba Hamid Karzai Na Afghanistan