VOANews.com

 
Labarai Cikin Harsuna 45
Iran Ta Yi Gwajin Makamai Masu Linzami

29/09/2009
Harba Shahab-3 a kusa da Qom, kudu da Teheran
Harba makamin Shahab-3 Ranar 27 Satumba 2009
Iran ta ce ta samu nasarar gwajin biyu daga cikin makamanta masu linzami da suka fi cin dogon zango, wadanda masu fashin bakin harkokin tsaro suka ce su na iya kai wa kan Isra’ila ko kudancin Turai.

Jiya litinin, gidan telebijin na Iran ya nuna tashin makami mai linzami samfurin Shahab na Uku cikin kura a wata hamada. An yi imanin cewa wannan makami mai linzami da ake harbawa daga doron kasa zuwa doron kasa yana iya cin kilomita dubu 2.

Wakilan Britaniya da Faransa da Jamus da kuma Tarayyar Turai sun bayyana damuwa kan wannan gwajin. Fadar shugaban Amurka ta White House ta bayyana gwajin a zaman "tsokana" ta kuma bukaci hukumomin Iran da su kyale sufetoci su shiga cikin sabuwar masana’antar tace man nukiliya ta Iran da aka gano ba tare da tsangwama ba.

Ministan harkokin wajen Rasha, Sergei Lavrov, ya bayyana gwaje-gwajen a zaman abin "damuwa." Kamfanonin dillancin labarai na Rasha sun ambace shi yana kira ga Iran da ta bayar da cikakken hadin kai ga sufetocin nukiliya na Majalisar Dinkin Duniya.

Amurka da sauran manyan kasashen duniya zasu matsa lamba kan kasar Iran da ta bayyana dukkan ayyukan nukiliyar da ta ke gudanarwa a wajen ganawar da zasu yi da ita ranar alhamis a birnin Geneva.


E-mail This Article Aika Labarin Nan ma Wani Ta E-Mail
Print This Article Shafi Mai Saukin Bugawa
  Muhimmin Labari
Jami'an Sojan Iran Sun Ce An fara Wata Gagarumar Rawar Daji Ta Kare Kasa Daga Hari Ta Sama

  Karin Labarai
Yau Litinin Majalisar Dinkin Duniya Zata Kaddamar Da Aiki Mafi Girma Na Rigakafin Cutar Shawara Da Ta Taba Yi
Kwallon Kafa Ya Haddasa Rikicin Diflomasiyya Tsakanin Masar Da Aljeriya
Somaliyawa 'Yan Fashi A Teku Sun Sake Kai Hari Kan Wani Jirgin Ruwan Amurka Da Suka Taba Kamawa
Yau Alhamis Za A Rantsar Da Shugaba Hamid Karzai Na Afghanistan