VOANews.com

 
Labarai Cikin Harsuna 45
Yau Talata Za A Fara Sake Kidaya Dukkan Kuri'un Shugaban Kasa A Gabon

29/09/2009

Supporters of Ali Bongo Ondimba, son of former dictator Omar Bongo, leave his final presidential campaign rally in Libreville, Gabon, 29 Aug 2009
Magoya Bayan Ali Ben Bongo a Libreville
A yau talata kotun tsarin mulki ta kasar Gabon zata fara sake kidaya dukkan kuri’un da aka kada a zaben shugaban kasa na ranar 30 ga watan Agusta. ‘Yan takarar da suka sha kaye a zaben ne suka bukaci da a sake kidayar, a bayan da dan takarar jam’iyya mai mulki, Ali Ben Bongo, ya samu gagarumar nasara.

'Yan adawa sun yi zargin cewa magoya bayan Bongo sun tabka magudi, su na kuma fatar sake kidaya kuri’un zai kai ga soke wannan sakamako. Amma akasarin masu fashin bakin siyasa sun ce zai yi matukar wuya sake kidaya kuri’un ya sauya sakamakon. Suka ce akasari an nuna gaskiya a lokacin zaben duk da dan abinda ba za a rasa ba.

Tarzoma ta barke na wani dan karamin lokaci a Libreville, babban birnin kasar, da kuma birnin Port Gentil, a bayan da aka bayyana sakamakon wannan zabe. Gwamnati ta ce an kashe mutane uku a tarzomar. 'Yan adawa suka ce wadanda suka mutu sun kai akalla 15.


E-mail This Article Aika Labarin Nan ma Wani Ta E-Mail
Print This Article Shafi Mai Saukin Bugawa
  Muhimmin Labari
Kwallon Kafa Ya Haddasa Rikicin Diflomasiyya Tsakanin Masar Da Aljeriya

  Karin Labarai
Somaliyawa 'Yan Fashi A Teku Sun Sake Kai Hari Kan Wani Jirgin Ruwan Amurka Da Suka Taba Kamawa
Yau Alhamis Za A Rantsar Da Shugaba Hamid Karzai Na Afghanistan
Switzerland Ta Doke Nijeriya A Wasan Karshe Na Cin Kofin Kwallon Kafar Duniya Na Samari
Dan Kunar-Bakin-Wake Ya Kai Farmaki Kan Hukumar Leken Asirin Pakistan