 |
Captain Moussa Dadis Camara
|
Shaidu
da jami’an kiwon lafiya sun ce an kashe mutane akalla hamsin da takwas a kasar
Guinea, a arangamar da aka yi a tsakanin dakarun tsaro da ‘yan adawa, wadanda
suka yi ko oho da haramcin gwamnati suka gudanar da zanga-zanga. An yi wannan
artabu jiya litinin a Conakry, babban birnin kasar. Wakiliyar
Muryar Amurka, Ricci Shryock, ta ambaci shaidu su na fadin cewa sojojin kurfau
sun yi harbi kan masu zanga zangar da suka yi gangami a babban filin wasa na
Conakry, domin nuna adawarsu da shirin shugaban gwamnatin mulkin soja, Kyaftin
Moussa Dadis Camara, na tsayawa takara a zaben da za a gudanar a kasar.
Dakaru
sun yi kokarin hana mutane shiga filin wasan a saboda gwamnatin mulkin soja ta
haramta duk zanga-zanga kafin bukukuwan tuna ranar samun ‘yancin kai da za a yi
ranar jumma’a. Amma wata gamayya ta kungiyoyin al’umma da jam’iyyun siyasa da
kungiyoyin kwadago sun ce allambaram sai sun yi gangami.
Shi
dai Camara ya kwace mulki a watan Disamba, ‘yan sa’o’i kadan a bayan mutuwar
shugaba Lansana Conte. Jim kadan bayan da ya kwace mulkin, yayi alkawarin cewa
zai gudanar da zabe na gaskiya kuma ba zai tsaya takara a zaben ba. Amma tun
bayan wancan lokacin, majalisar mulkin soja ta ce kowa na iya tsayawa takara.
Shi kansa Kyaftin Camara ya fada a watan da ya shige cewa ba zai kunyata magoya
bayansa dake ta nemansa ya tsaya takara ba.
Daga
can Abidjan kuma, wakilin Muryar Amurka Scott Stearns yace Kyaftin Camara yana
kokarin ya nisanta kansa da harbe mutane akalla 58 da jami’an tsaro suka yi
jiya litinin a Conakry.
Ya fadawa gidan
rediyon RFM na Senegal cewa bai ji dadi ba, da aka ba shi labarin mace-mace a
wajen gangamin masu yin adawa da tsayawarsa takara.
A
bayan kashe-kashe da raunukan da mutane suka samu a hannun jami’an tsaron, an
kuma kama shugabannin adawa aka dauke su zuwa babban barikin soja na Gini. Kyaftin
Camara yace ya tambayi halin da shugabannin adawar suke ciki, kuma an tabbatar
masa da cewar su na cikin koshin lafiya.
Zanga
zangar nuna kin jinin shiga takara da Kyaftin Camara ke shirin yi ita ce mafi
girma tun hawarsa kan mulki. Kuma ita ce mafi zub da jini. Ba za a iya tantance
zahirin yawan mutanen da suka mutu ba a saboda an ce sojoji su na kwashe
gawarwakin su na tafiya da su.