VOANews.com

 
Labarai Cikin Harsuna 45
Shugabannin Afirka Ta Yamma Zasu Yi Taron Koli Kan Guinea-Conakry

14/10/2009

Taron ECOWAS
TWani taron kolin ECOWAS a Ouagadougou a 2007
Shugabannin kasashen Afirka ta Yamma sun yarda zasu yi taron koli cikin wannan makon domin tattauna tankiyar siyasar da ta ke akwai a kasar Guinea-Conakry. Za a yi wannan taron kolin ranar asabar a Abuja, babban birnin Nijeriya, a ranar da ita ma Kungiyar Tarayyar Kasashen Afirka ta shirya ganawa domin tattauna yiwuwar kafa takunkumi a kan gwamnatin mulkin soja ta kasar Guinea.

An yi Allah wadarai da gwamnatin ta mulkin sojan Guinea, hagu da dama, a saboda wutar da sojojinta suka bude a kan masu zanga-zangar nuna kin jinin gwamnati a ranar 28 ga watan Satumba.

Majalisar Dinkin Duniya, MDD, da wata kungiyar kare hakkin bil Adama ta kasar sun ce an kashe mutane dari da hamsin da bakwai. Gwamnati Guinea ta ce mutane hamsin da bakwai na kai kawai aka kashe, ta kuma ce akasarinsu an tattake su ne suka mutu lokacin da mutane ke ribibin fita daga filin wasan Conakry, babban birnin kasar.

Jiya talata, titunan babban birnin sun kasance wayam a rana ta biyu ta yajin aikin gidan kowa da shi da aka shirya domin tunawa da wadanda aka kashe. Kungiyoyin kwadago ne suka shirya wannan yajin aiki na kwana biyu domin jimamin wadanda suka mutu.



E-mail This Article Aika Labarin Nan ma Wani Ta E-Mail
Print This Article Shafi Mai Saukin Bugawa
  Muhimmin Labari
Kwallon Kafa Ya Haddasa Rikicin Diflomasiyya Tsakanin Masar Da Aljeriya

  Karin Labarai
Somaliyawa 'Yan Fashi A Teku Sun Sake Kai Hari Kan Wani Jirgin Ruwan Amurka Da Suka Taba Kamawa
Yau Alhamis Za A Rantsar Da Shugaba Hamid Karzai Na Afghanistan
Switzerland Ta Doke Nijeriya A Wasan Karshe Na Cin Kofin Kwallon Kafar Duniya Na Samari
Dan Kunar-Bakin-Wake Ya Kai Farmaki Kan Hukumar Leken Asirin Pakistan