VOANews.com

 
Labarai Cikin Harsuna 45
Yau Miliyoyin Musulmi Mahajjata Suke Hawan Arafat, Yayin Da Ruwan Sama Ya Kashe Mutane 11

26/11/2009

[insert caption here]
Aikin Hajji
Ruwan sama kamar da bakin kwarya da kuma ambaliyar da ya haddasa, sun kashe mutane akalla 11 jiya laraba a Sa’udiyya, a yayin da miliyoyin Musulmi suka shiga haramar fara aikin Hajjin bana.

Ruwan da aka shafe tsawon rana jiya laraba ana tabkawa, ya kawo ambaliya a kan tituna, ya haddasa cunkoson ababen hawa, ya katse wutar lantarki, ya kuma sa mutane suka kasa fita daga cikin gidajensu. Wasu mahajjatan sun kasa samun hanyar wucewa a yayin da suka doshi birni mai Tsarki na Makka daga birnin Jeddah.

Mutanen da suka samu isa wurare masu tsarki ba su kai na shekarun baya ba ya zuwa jiya larabar.

A jiyan, mahajjata cikin harami sun yi dawafi a dakin Ka’abah mai tsarki. Ana sa ran mahajjata miliyan biyu da rabi ne zasu yi aikin Hajjin bana, yayin da hukumomi suke aiki ka’in da na’in don kawar da damuwa game da cutar murar aladu da kuma tsaron lafiyar mahajjatan.

Shugaba Barack Obama na Amurka ya bada sanarwa jiya laraba, yana mika sako na fatar alheri ga Musulmin dake aikin Hajji a Sa’udiyya tare da taya illahirin Musulmi na duniya murnar Sallar layya da za a yi kwana guda bayan hawan Arafat.

Shi ma babban kwamandan sojojin Amurka da na NATO a Afghanistan, Janar Stanley McChrystal, ya aike da sakon Barka da Sllah ga Musulmi ya kuma yi kira ga al’ummar Afghanistan da su yi aiki da akidojin addinin Musulunci kamar gaskiya, da halin kwarai da adalci da kuma ‘yanci don sake gina kasar Afghanistan.


E-mail This Article Aika Labarin Nan ma Wani Ta E-Mail
Print This Article Shafi Mai Saukin Bugawa
  Muhimmin Labari
Sakatariyar Harkokin Wajen Amurka Hillary Clinton Tace Barazanar Masu Matsanancin Raayin Islama Kan Amurka Ta Fi Ta Shirin Nukiliyar Iran Da Koriya Ta Arewa

  Karin Labarai
Majalisar Dinkin Duniya Tana Bin Bahasin Zargin Laifukan Yaki Da Take Zargin Israila Da Hamas
Tarayyar Afirka Zata Ladabtar Da Duk Wadanda Suka Shirya Juyin Mulkin Soja Cikin Ko Wace Kasa A Nahiyar
Najeriya Tana Shirin Sayar da Wani Kaso  Daga Rijiyoyin Mai Dake Doron Kasa Da Cikin Teku
Shugaba Barack Obama Ya Gabatarda Jwabin Rahoton Hali Da Kasa Ke Ciki Na Farko Tun Kama Aikinsa
An Kai Hari Kan Babban Bututun daukar Mai Na Shell A Yankin Niger Delta
Malawi Ta Karbi Shugabancin Tarayyar Afirka Bayan Yunkurin Qaddafi Na Neman Tazarce Ya Faskara
Shugaban Amurka Barack Obama Ya Gabatar Da Kasafin Kudi Na Shekara Mai Zuwa
Majalisar Ministocin Najeriya Ta Ce Shugaba Yaradua Yana Karfin Ci Gaba Da Gudanarda Aikinsa Duk Tafiyar Neman Jinya
Ana Zaman Dar Dar A Sokoto Bayan Yan Banga Sun Kashe Mutum Daya Suka Kona Gida a Unguwar Tudunwada
Alqaida Tana Gargadin Cewa Zata Ci Gaba Da Kai Hari Kan  Muradun Amurka  Idan Amurkan Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Isra'ila
Ana Baza Jita Jitar Sojoji A Najeriya Suna Shirya Juyin Mulki
Za A Yi Taron Kolin Tarayyar Afirka Makon Gobe Qaddafi Yana Shirin Tazarce A Shugabancin Kungiyar
Majalisar Dattijai Ta Najeriya Ta Yi Muhawara Kan Rashin lafiyar Shugaba Yaradua
Kotun Najeriya ta bada wa'adin tabbatar da lafiyar shugaba Yar'adua.
Kungiyar Lauyoyi Ta Najeriya Ta Nemi Kotu Ta Baiwa Mataimakin Shugaban Kasa Shugabanci Na Wucin Gadi
GWAMNATI TA SASSAUTA DOKAR HANA FITA A YAYIN DA SOJOJIN NAJERIYA KE SINTIRI A GARIN JOS
Gwamnatin Jihar Yobe Ta kafa Dokar Hana Aure Ba Tareda An Auna Jini Ba
Sojoji Suna Ci Gaba Da Sintiri A Jos Da Kewaye
SOJOJIN NAJERIYA NA KOKARIN KASHE WUTAR RIKICIN DA YA BARKE A JOS, JAHAR FILATO
Hukumomin Nigeria Sun Bada Labarin Asarar Rayuwa Ta Farko Da Aka Taba Rasawa A Sanadin Cutar Murar Aladu Ta H1n1. A Yau Ne Ma’aikatar Lafiya Ta Nigeria Ta Bada Labarin Cewa Wata Mace, 38 Mazauniya Lagos Da Ta Kamu Da Cutar, Ta Mutu A Ran 5 Ga Watan Nan Na
Jamiyyar Democrat Ta Sha  Kaye A Zaben Cike Kujerar Marigayi Edward Kennedy A Jihar Massachussetts
Mataimakin Shugaban Nigeria Goodluck Jonathan Yau Ya Umurci Tura Sojoji Zuwa Jos Fadar Gwamnatin Jihar Pilato Inda Mummunan Rikicin Addini Ya Barke Tsakanin Musulmi da Kirista.
Yau Litinin Hutu Ne A Amurak Domin Karrama Gwarzon Yaki Da Wariya
Shan Taba Sigari a Afrika  Audio Clip Available
Yan Kungiyar Taliban Sun Kai Hari Kan Gine Ginen Gwamnati A Kabul
Kungiyoyin Hamayya  A Iran Suna Kira Da A Yi Zanga Zanga Ranar Bikin Yujin Juya Hali
An kafa Dokar Hana Yawo Bayan Barkewar Sabon Rikicin Addini A Jos
Kakakin Umaru Musa 'Yar'aduwa Yace Shugaban Yana Nan Da Rai
'Yan Wasan Togo Zasu Koma Gida
Bai Kamata Amurka Ta Ba Umar Farouk Abdulmutallab Lauya Ba...
An Kashe Dan Jaridar Britaniya  A Afghanistan
Shugaba Obama Ya Nemi Karin Hadin Kai Da Kasashen Musulmi Wajen Inganta Tsaron Jiragen Fasinja