VOANews.com

 
Labarai Cikin Harsuna 45
Daga Mai Neman Koyan Hausa Na Zamo Babbar Mai Sha'awar Fina-Finai Da Wakokin Hausa

03/11/2009

Talatu Baturiya da Ibrahim Alfa Ahmed mai gabatar ad shirin
Talatu Baturiya da Ibrahim Alfa Ahmed mai gabatar da shirin
(An sabunta wannan labari da kashi na 2 da na 3 na hira da Carmen McCain)

Watakila idan ka ce Carmen McCain, mutane da yawa ba za su san ko maganar wa ka ke yi ba, amma da zarar ka ce Talatu Danny ko kuma Talatu Baturiya, to nan da nan za ka ji an ce to, Talatu kake nufi? Musamman ga masu shiryawa, ko tsarawa ko fitowa a fina-finan Hausa da mawakan zamani na Hausa, wannan suna ya zamo kamar abin nan da Hausawa ke kira "Gidan kowa da shi."

A yanzu dai, Talatu, daliba a Jami'ar Wisconsin dake garin Madison, tana rubuta takardunta na samun babban digiri na digirgir, ko PhD, a kan fina-finan Hausa da kuma wakoki na zamani da suka zamo ruwan dare a kasar Hausa a wannan lokacin.

Carmen McCain (sunan Talatu na asali ke nan idan ba mantawa aka yi ba) ta fara zuwa Nijeriya tun shekarar 1988, lokacin tana mai shekaru 11 da haihuwa, tare da iyayenta, wadanda har yanzu su na Nijeriya su na koyarwa a Jami'ar Jos. A nan ta fara haduwa da harshen Hausa, ta kuma fara nuna sha'awar wannan harshe.

A cikin hirar da muka yi da ita don filin "A Bari Ya Huce..." malamar ta bayyana yadda ta tafi Sakkwato don koyon harshen Hausa, ta kuma koma Kano domin kara zurfafa wannan nazari nata na adabin Hausa.

Ta ce ta fara kallon fina-finan Hausa a kokarin koyon harshe da kuma al'adun Hausawa, amma nan da nan sai ta kamu da sha'awar wadannan fina-finai da kuma wakokin da ake yi cikinsu har ta zo ga yanke shawarar yin nazari mai zurfi a kan wannan.

A kashin farko na wannan hira da za a iya ji a gefen dama a sama, Talatu ta yi maganar yadda ta fara sha'awar wannan harshe da fina-finai. A yi sauraro lafiya.


Download Hira Da Talatu Baturiya
Yi Kwafi  (MP3)
Listen to This Report Hira Da Talatu Baturiya
Saurara (MP3)
Download Hira Da Talatu Baturiya 2
Yi Kwafi  (MP3)
Listen to This Report Hira Da Talatu Baturiya 2
Saurara (MP3)
Download Hira Da Talatu Baturiya 3
Yi Kwafi  (MP3)
Listen to This Report Hira Da Talatu Baturiya 3
Saurara (MP3)
E-mail This Article Aika Labarin Nan ma Wani Ta E-Mail
Print This Article Shafi Mai Saukin Bugawa
  Muhimmin Labari
Sakatariyar Harkokin Wajen Amurka Hillary Clinton Tace Barazanar Masu Matsanancin Raayin Islama Kan Amurka Ta Fi Ta Shirin Nukiliyar Iran Da Koriya Ta Arewa

  Karin Labarai
Majalisar Dinkin Duniya Tana Bin Bahasin Zargin Laifukan Yaki Da Take Zargin Israila Da Hamas
Tarayyar Afirka Zata Ladabtar Da Duk Wadanda Suka Shirya Juyin Mulkin Soja Cikin Ko Wace Kasa A Nahiyar
Najeriya Tana Shirin Sayar da Wani Kaso  Daga Rijiyoyin Mai Dake Doron Kasa Da Cikin Teku
Shugaba Barack Obama Ya Gabatarda Jwabin Rahoton Hali Da Kasa Ke Ciki Na Farko Tun Kama Aikinsa
An Kai Hari Kan Babban Bututun daukar Mai Na Shell A Yankin Niger Delta
Malawi Ta Karbi Shugabancin Tarayyar Afirka Bayan Yunkurin Qaddafi Na Neman Tazarce Ya Faskara
Shugaban Amurka Barack Obama Ya Gabatar Da Kasafin Kudi Na Shekara Mai Zuwa
Majalisar Ministocin Najeriya Ta Ce Shugaba Yaradua Yana Karfin Ci Gaba Da Gudanarda Aikinsa Duk Tafiyar Neman Jinya
Ana Zaman Dar Dar A Sokoto Bayan Yan Banga Sun Kashe Mutum Daya Suka Kona Gida a Unguwar Tudunwada
Alqaida Tana Gargadin Cewa Zata Ci Gaba Da Kai Hari Kan  Muradun Amurka  Idan Amurkan Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Isra'ila
Ana Baza Jita Jitar Sojoji A Najeriya Suna Shirya Juyin Mulki
Za A Yi Taron Kolin Tarayyar Afirka Makon Gobe Qaddafi Yana Shirin Tazarce A Shugabancin Kungiyar
Majalisar Dattijai Ta Najeriya Ta Yi Muhawara Kan Rashin lafiyar Shugaba Yaradua
Kotun Najeriya ta bada wa'adin tabbatar da lafiyar shugaba Yar'adua.
Kungiyar Lauyoyi Ta Najeriya Ta Nemi Kotu Ta Baiwa Mataimakin Shugaban Kasa Shugabanci Na Wucin Gadi
GWAMNATI TA SASSAUTA DOKAR HANA FITA A YAYIN DA SOJOJIN NAJERIYA KE SINTIRI A GARIN JOS
Gwamnatin Jihar Yobe Ta kafa Dokar Hana Aure Ba Tareda An Auna Jini Ba
Sojoji Suna Ci Gaba Da Sintiri A Jos Da Kewaye
SOJOJIN NAJERIYA NA KOKARIN KASHE WUTAR RIKICIN DA YA BARKE A JOS, JAHAR FILATO
Hukumomin Nigeria Sun Bada Labarin Asarar Rayuwa Ta Farko Da Aka Taba Rasawa A Sanadin Cutar Murar Aladu Ta H1n1. A Yau Ne Ma’aikatar Lafiya Ta Nigeria Ta Bada Labarin Cewa Wata Mace, 38 Mazauniya Lagos Da Ta Kamu Da Cutar, Ta Mutu A Ran 5 Ga Watan Nan Na
Jamiyyar Democrat Ta Sha  Kaye A Zaben Cike Kujerar Marigayi Edward Kennedy A Jihar Massachussetts
Mataimakin Shugaban Nigeria Goodluck Jonathan Yau Ya Umurci Tura Sojoji Zuwa Jos Fadar Gwamnatin Jihar Pilato Inda Mummunan Rikicin Addini Ya Barke Tsakanin Musulmi da Kirista.
Yau Litinin Hutu Ne A Amurak Domin Karrama Gwarzon Yaki Da Wariya
Shan Taba Sigari a Afrika  Audio Clip Available
Yan Kungiyar Taliban Sun Kai Hari Kan Gine Ginen Gwamnati A Kabul
Kungiyoyin Hamayya  A Iran Suna Kira Da A Yi Zanga Zanga Ranar Bikin Yujin Juya Hali
An kafa Dokar Hana Yawo Bayan Barkewar Sabon Rikicin Addini A Jos
Kakakin Umaru Musa 'Yar'aduwa Yace Shugaban Yana Nan Da Rai
'Yan Wasan Togo Zasu Koma Gida
Bai Kamata Amurka Ta Ba Umar Farouk Abdulmutallab Lauya Ba...
An Kashe Dan Jaridar Britaniya  A Afghanistan
Shugaba Obama Ya Nemi Karin Hadin Kai Da Kasashen Musulmi Wajen Inganta Tsaron Jiragen Fasinja